Friday, December 5, 2008

AISHA ZAKARI




Aisha Zakari 'yar asalin Hadejia, fitacciyar marubuciya ce, kodayake ta fi karfi a rubutun turanci daga baya ta fara rubutun Hausa. Ta samu digirinta na farko a fanning Labarin Kasa (Geography) daga Jamiár Bayero ta Kano kuma tana cikin wadanda suka rubuta wani wasan kwaikwayo na gidan Radiyon BBC watau Gatanan Gatananku ta kuma rubuta waken turanci da dama wadanda aka buga a litattafai da kuma gidajen yana. Ta taba zama Magatakardar Kudi ta Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) ta Kasa kuma ta rike mukamai a ANA Kano da dama hard a na Mataimakiyar Shugaba. Aisha Fellow ce ta Leadership Development Mechanism (LDM Fellow) kuma tana daya daga cikin hazikan matasa da suka taimakawa adabin Hausawa da Hausawa kuma a halin yanzu tana zaune da mijinta a Amurka inda take ci gaba da karatu.
Littafinta da ta rubuta ko ta fito a ciki sun hada da:
Himma Ba Ta Ga Raggo
Verses in Absentia Poetry of Aisha Usman Bugaje (Coeditor)
Pregnant Skies: Anthology of 50 Nigerian Poets
Mazan Fara: ANA Zamfara Anthology of Poems and Short Stories

1 comment:

Idris Ibrahim Kubau said...

Alhamdulillahi na karu game da tarihi da Rayuwar A'isha Zakari. Na san ta da kokari wajen ci gaba da kyautata Rayuwar al'umma.

Hajiya A'isha Zakari tana da son mutane da zamantakewa tare da mutane. Ta iya mu'amala da jama'a sosai, tana da hakuri da son taimakawa jama'a.

Allah Ya bada sa'a Ya karawa rayuwa albarka.