An haifi Hajiya Hafsatu a Birnin Kano. Ta yi karatunta na boko a Kano kafin ta yi aure ta koma Gusau da zama. Fitacciyar marubuciyar Hausa ce wadda littafinta na So Aljannar Duniya shi ne littafin zube na farko da mace ta rubuta a harshen Hausa. Ta wallafa 'Yardubu Mai Tambotsai da kuma Saba Dan Sababi. Tana kuma rubutu da turanci da kuma fillanci. Marubuciya ce wadda ke da kishin rubutu ta kan kuma halarci tarurrukan marubutan Hausa da na Nijeriya. Bayan rubutu takan taba siyasa don ta taba takarar Gwamna a jihar Zamfara.
No comments:
Post a Comment