Wannan dandali ne aka yi na musamman don samar da bayanai game da Marubutan Hausa. Za mu samar da bayanai akan tarihinsu da rubuce-rubucensu da ma hotunansu. Kuma za mu rika kawo labarai har ma da hotuna da suka shafi Marubutan Hausa. A sha karatu lafiya.
Wednesday, February 24, 2010
FATIMA UBA ADAMU (ZAHRA)
An haifi Fatima Uba Adamu a Kano. Ta yi karatun Firamare a Tarauni Special Primary School daga 1988-1994, ta yi Sakandare a Makarantar Sakandaren 'Yanmata ta Kabo daga 1996-2001. Daga 2002 zuwa 2006 ta yi digirinta na farko a fannin Hausa, a halin yanzu tana digirinta na biyu tare da kwarewa a fannin Adabin Hausa. Ta kuma yi difiloma a fannin kwamfyuta. Ta dan taba aiki da jaridar Daily Trust kafin ta koma karatunta na digiri na biyu. Littafinta na farko shi ne Kaddara Da Zabi.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment