Saturday, June 13, 2009

UMMA ADAMU


An haifi Umma Adamu ranar 15th ga Oktoba 1981 a Gwarzo, duk da cewa ita 'yar asalin Hadejia ce. Ta yi karatun Firamare a Kanti Primary School Kazaure daga 1987-2003. Ta kuma yi karatun

Sakandare a Malam Madori da Sakandaren Kimiyya ta Taura inda ta gama a 1999. Ta ci gaba da karatu daga 2000 a School of Health Technology Jahun da Informatics Institute Kazaure da kuma Jigawa State College of Education har zuwa 2006. A halin yanzu (2009) tana karatu ne a Kano State University of Science and Technology Wudil. Cikin litattafan da ta buga sun hada da:

1. Raino, 2. Rigakafi 3. Sirrinus ko Sirrimu 4. Wahayi 5. Zaman Jira 6. Ya Zalince ni 7. Sabanin Ra'ayi 8. Abu a Duhu.

Tana sha'awar koyarwa da kallon fina-finai da tafiye-tafiye da koyarwa da kuma rubuta kirkirarrun labaru.

1 comment:

pokyes kavwam said...

Enter your comment...akwai yadda zana iya yin magana da ita? ina bukatan littatafen ta