Sunday, February 22, 2009

ABDULLAHI MUKHTAR (YARON MALAM)


An haife shi ranar 1/6/76 a unguwar Fagge. Ya yi makarantar Fagge Special Primary School Ibrahim Taiwo Road. Daga nan suka koma Birged da zama inda ya karasa firamare a Birged Special primary School. Ya shiga Aliyu Bn Abu Talib School daga 1991-1996. Daga nan ya koma makarantar zaure don ci gaba da karatun addini zuwa 2005. A 2005 ne ya yi karatun Professional Diploma a BUK.
Litattafansa na Hausa sun hada da:
Bajakade
Mayakiya
Bakin Gumurzu
Gimbiya Assadatu
Artabu
Gumu
Tunga
Bajakadiya'(Ýar Mai ganye)
Sihirtacciya
Yahudu Badda Musulmi
Tsibirin Bamuda
Yakau
Sirrin Aure da Maáurata A Muslunci
Duniyar Maáurata A Muslunci
Ku Tambayeni Kafin Ku Rasa Ni
Kuriá
Hukunce-Hukuncen Jinin Haila
Hassada da Maganinta A Muslunci
Kissoshin Ahlul Baiti

Friday, February 20, 2009

ZAHARADDEEN IBRAHIM KALLAH


Zaharaddeen Ibrahim Kallah ya yi digirinsa a kan ilimin zamantakewar dan Adam da kuma siyasa. Marubuci ne da yake rubutu a harsuna guda biyu, hausa da turanci. Ya taba lashe gasar rubutun waka ta turanci ta duniya a shekara ta 2004, da Negerian.Biz suka shirya. Yana daga cikin shugabanni gudanarwa na ANA. A hali yanzu yana aiki da Strategic Planning a Jami’ar Bayero ta Kano. Ya rubuta littafin Karkon Dabino sannan ya fito a littafai na gamayya da suka hada da Five hundred Nigerian poets, da Mazan Fara. Littafansa da suke hanyar fitowa sun hada da So ko Wahala da Usman Mai duniya da Lokaci Bako ne da Love in Mayuwandu tare da The Right Choice.