An haife shi ranar 1/6/76 a unguwar Fagge. Ya yi makarantar Fagge Special Primary School Ibrahim Taiwo Road. Daga nan suka koma Birged da zama inda ya karasa firamare a Birged Special primary School. Ya shiga Aliyu Bn Abu Talib School daga 1991-1996. Daga nan ya koma makarantar zaure don ci gaba da karatun addini zuwa 2005. A 2005 ne ya yi karatun Professional Diploma a BUK.
Litattafansa na Hausa sun hada da:
Bajakade
Mayakiya
Bakin Gumurzu
Gimbiya Assadatu
Artabu
Gumu
Tunga
Bajakadiya'(Ýar Mai ganye)
Sihirtacciya
Yahudu Badda Musulmi
Tsibirin Bamuda
Yakau
Sirrin Aure da Maáurata A Muslunci
Duniyar Maáurata A Muslunci
Ku Tambayeni Kafin Ku Rasa Ni
Kuriá
Hukunce-Hukuncen Jinin Haila
Hassada da Maganinta A Muslunci
Kissoshin Ahlul Baiti