Wednesday, February 24, 2010

FATIMA UBA ADAMU (ZAHRA)


An haifi Fatima Uba Adamu a Kano. Ta yi karatun Firamare a Tarauni Special Primary School daga 1988-1994, ta yi Sakandare a Makarantar Sakandaren 'Yanmata ta Kabo daga 1996-2001. Daga 2002 zuwa 2006 ta yi digirinta na farko a fannin Hausa, a halin yanzu tana digirinta na biyu tare da kwarewa a fannin Adabin Hausa. Ta kuma yi difiloma a fannin kwamfyuta. Ta dan taba aiki da jaridar Daily Trust kafin ta koma karatunta na digiri na biyu. Littafinta na farko shi ne Kaddara Da Zabi.

Thursday, February 4, 2010

Marubutan Hausa a Yamai

Wannan hoton Dr Yusuf Adamu ne (dama) da Ado Ahmad Gidan dabino (Hagu) suka yi shigar buzaye a lokacin da suka kai ziyara Yamai da marubutan Hausa na Nijeriya.

FARFESA IBRAHIM MALUMFASHI

Farfesa Ibrahim Malumfashin na daga cikin fitattu kuma Zakakuran manazartan Adabin Hausa.