Monday, October 19, 2009

TA'AZIYYAR HADI ABDULLAHI ALKANCI



Hagu zuwa dama: Danjuma Katsina, Hadi Alkanci, Yusuf Adamu a wani taro a Kano


Allah ya yi wa Marubuci Hadi Abdullahi Alkanci rasuwa ranar Litinin 12 ga Oktoba 2009 a Sakkwato bayan ya sha fama da rashin lafiya. Rasuwar Alkanci babban rashi ne ga marubuta da manazarta da ma al'umar Nijeriya. Allah ya jikansa da gafara ya kuma albarkaci bayansa.
Bayan sanarwar da na yi a dandalin marubuta kamar haka:

Salam,Ina bakin cikin sanar da ýan uwa cewa Allah ya yi wa Hadi Abdullahi Alkanci rasuwa jya da yamma a Sakkwato, ya yi fama da rashin lafiya wajen watannin uku, mun yi rashi babba, muna kuma rokon Allah ya gafarta masa ya kuma jikansa da rahma amin. Muna rokon yan uwa su yi masa addu'a koyaushe, ga dan takaitaccen tarihinsa nan a wannan rariyar likau
http:// marubutanhau sa.blogspot. com/2008/ 09/hadi-abdullah i-alkanci. html

Allah ya gafarta masa ya kuma sa mu ma mu cika da imani amin. Dr Yusuf Adamu

Mun samu sakwannin taáziyya da dama, ga kalilan daga cikinsu a kasa:

Ado Ahmad Gidan Dabino
ALLAH AKBAR, Allah ya ji kan Hadi Abdullahi Alkanci. Marubucin Soyayya Ta Fi Kudi (littafin wasan kwaikwayo) da Harsashin Kasa da Shin So Gaskiya Ne? da sauran su. Babu shakka mun yi babban rashi a fagen marubuta, haziki gwarzo a fagen fasaha ya tafi.

Ba zan manta da haduwa ta ta karshe da Hadi ba a lokacin da ya zo Kano wajen bikin kaddamar da littattafan Bashir Othman Tofa, yana cikin mutanen hudu da na yi hira da su a ciki shirin da nake gabatarwa a gidan rediyo FREEDOM mai suna Alkalami Ya Fi Takobi, mutane sun yaba da ire-iren bayanan da ya yi sosai, kuma in yana magana lallai ka san cikakken mutumin Sokoto ne, mai iya karin magana da dabarun zance.Lokacin da na ji labarin rasuwarsa ta hanyar SMS daga Yusuf Adamu ina jihar Lagos, ba shakka na kadu sosai da ganin wannan sakon.

ALLAHU AKBAR! ALLAHU !! AKBAR!!! Allah ka rahamshe shi, ka sa ya huta, mu kuma Allah ya kyauta tamu in ta zo. Allah ka sa gidan Aljanna ce makomarmu baki daya. Amin!!! Ina mika sakon gaisuwa ga dukkanin 'yan'uwa da abokan arziki da dukkan Sakkwatawa.


***
JAMILU NAFSENCIBIYAR LAFAZIN HAUSA
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJI' UN....Aduk sa'ilin da muka ji wannan kalma tuni take mana nuni da wani gagarumin abu ne ya auku.hakanne yasa nima ina samun wannan rashin jangwarzo mai bada gudunmawa musamman aharkar wasanni, abunda na iya furtawa kenan tare da tawassali da cewa muma tamu tananan zuwa. sai dai muce ubangiji ya kai rahma agareshi. mu kuma Allah yasa mu cika da imani, amin.

*****
Mamane Sahabi Ousmane Alias M.SONiamey Niger
Allahu akbar haka ne, Allah yaji kanshikuma ya sa, ya huta.abida ya bari Allah yabasu hakurida masoya da kuma yan uwa. mu kuma da muka rage in tamu ta zoAllah ya sa, mugama da iskan duniya lafiya Amin.ita rayuwa haka take, kowa lokacin shi, zai jira.ba'a gaggauta wa kowa, kuma ba'a jinkirta wa kowa. kulli nafsi za'ikatil mautko wace rai! sai ta dan-dana mutuwa.gaba dayan mu, muci gaba da yi wa junan mu, addu'a.intamu ta zo, Allah ya sa mucika da kalmar La'ilaha illallah Muhammadu Rasulullah.

******

Sarkin yan Nijar,
Atta Oumaten
إنا لله وانا اليه راجعون منهـا خلقناكم وفيهـا وعيدكم ومنهـا نخرجكم تارةاخرى
Dawannan nake meka tsakon ta'aziyar daukacin yan Nijar dake cikin wadannan zauruka, ga iyalai da abokan arziki na wannan ba wan Allah, allah yasa ya huta mu kuma idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani.
***
Uba Dan Zainab
Allah yayimasa rahama yasada shi da annabi sallalahu alaihi wasallamzuriyarsa kuma Allah yashiga lamuransu yasakasu bin surad'al mustaqeem.

****
Ahmad Yahuza Getso (B.A. MIAD, MPPA, HPDCS)
Allah ya gafarta masa ya kyautata tamu.
***
Muhammad Muhammad
Allah ya gafarta masa, mu kuma Allah ya kyauta karshen mu.
***
Isa Muhammad Inuwa
Allah Ya jikan Babban Marubuci Hadi Alkanci, Ya sa mutuwa hutu, Ya kyauta namu zuwan, Ya sa mu je a sa'a. Amin!

****
Muhammad Mansoor
Allah ya sa ya huta amin suma amin.
****
Ibrahim Sheme
Allah Ya jikanshi, ya yi masa rahama. Allahu Akbar! One of the last Titans of Classic Hausa Literature. Wallahi mun yi rashi.
****
Bala Muhammad (A Daidaita Sahu)
Innalillahi Wa inna Ilaihir Raji'un. Allah ya jikansa ya gafarta masa. In tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani, amin.

****
Aisha Zakari
Allah ya jikansa ya gafarta masa, lallai kam mun yi babban rashi.
****
Dr Wale Okediran (ANA President)
May his soul rest in perfect peace, amin.
***
Danjuma Katsina
A gaskiya mun yi rashi babba, Allah ka jikan wannan bawa naka ka gafarta masa amin.
***
Alhaji Kabiru Katsina
Allah ya gafarta masa, mun yi rashin jagora a rubutu.
***
Dr. Aliya Adamu
Allah ya Jikansa ya gafarta masa amin.

NASIRU G AHMAD YANAWAKI

An haifi Nasiru G. Ahamd a unguwar ‘Yan Awaki cikin Birnin Kano, ran 6 ga Safar, 1384, BH. (4/2/1964). Bayan karatun Alkur’ani, ya yi makarantar Firamare Islamiyya ta ‘Yan Awaki, daga 1975-1981. Ya wuce zuwa makarantar Nazarin Addinin Musulunci mai zurfi ta Shahuci (1981-1985). Sai Makarantar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Aminu Kano, (1986-1989) inda ya samu diploma a Harsunan Hausa da Larabci da Nazarin Addinin Musulunci. Daga (1993-1996), ya je Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo ta Sakkwato, inda ya samu digirin farko a harshen Hausa.
A shekarar 1984, ya halarci ajin koyon buga keken rubutu (Typewriting) da ke karkashin Hukumar Yada Ilimin Manya ta Kano, a 1992, ya halarci wani kwas da Jami’ar Musulunci ta Madina ke shiryawa, don horar da malaman Arabiyya da addinin Musulunci, a Jami’ar Bayero ta Kano. A 1992 din dai, ya je wani kwas na addinin Musulunci, a garin Idah, cikin jihar Kogi. A 1999, ya yi wani kwas na karatun gida, karkashin “Sincere Writers Club”, inda ya samu takardar shaida (certificate) kan aikin jarida.
A 1991, ya je jihar “Cross Rivers” inda ya yi aikin jami’i mai duba Malaman Kidaya (Supervisor). Ya koyi sarrafa na’ura mai kwakwalwa a aikace, (Practical) a “Urgent Computers” inda ya taba yin aiki. Yana cikin masu duba wakar Hausa, ta jarrabawar ‘W.A.E.C.’ Wakili ne na jaridar “People And Events”. Editan littattafai ne mai zaman kansa. Ya yi aikin koyarwa a makarantu da dama, (Firamare da Sakandare) tun daga 1984 zuwa yanzu. Yana da sha’awar ziyarce-ziyarce da kulla abota, da karance-karance a kowane fannin ilimi da rayuwa. Ya rubuta litattafai da dama, da wakoki jingim. Nasiru kuma na cikin Sahún gaba na ‎ ‘yan Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen jira Kano. A halin yanzu yana karatun digirinsa na biyu a Jamiár Ahmadu Bello (ABU) Zaria.