An haifi Fatima Uba Adamu a Kano. Ta yi karatun Firamare a Tarauni Special Primary School daga 1988-1994, ta yi Sakandare a Makarantar Sakandaren 'Yanmata ta Kabo daga 1996-2001. Daga 2002 zuwa 2006 ta yi digirinta na farko a fannin Hausa, a halin yanzu tana digirinta na biyu tare da kwarewa a fannin Adabin Hausa. Ta kuma yi difiloma a fannin kwamfyuta. Ta dan taba aiki da jaridar Daily Trust kafin ta koma karatunta na digiri na biyu. Littafinta na farko shi ne Kaddara Da Zabi.
Wannan dandali ne aka yi na musamman don samar da bayanai game da Marubutan Hausa. Za mu samar da bayanai akan tarihinsu da rubuce-rubucensu da ma hotunansu. Kuma za mu rika kawo labarai har ma da hotuna da suka shafi Marubutan Hausa. A sha karatu lafiya.
Wednesday, February 24, 2010
FATIMA UBA ADAMU (ZAHRA)
An haifi Fatima Uba Adamu a Kano. Ta yi karatun Firamare a Tarauni Special Primary School daga 1988-1994, ta yi Sakandare a Makarantar Sakandaren 'Yanmata ta Kabo daga 1996-2001. Daga 2002 zuwa 2006 ta yi digirinta na farko a fannin Hausa, a halin yanzu tana digirinta na biyu tare da kwarewa a fannin Adabin Hausa. Ta kuma yi difiloma a fannin kwamfyuta. Ta dan taba aiki da jaridar Daily Trust kafin ta koma karatunta na digiri na biyu. Littafinta na farko shi ne Kaddara Da Zabi.
Thursday, February 4, 2010
Marubutan Hausa a Yamai
Monday, October 19, 2009
TA'AZIYYAR HADI ABDULLAHI ALKANCI

Bayan sanarwar da na yi a dandalin marubuta kamar haka:
Salam,Ina bakin cikin sanar da ýan uwa cewa Allah ya yi wa Hadi Abdullahi Alkanci rasuwa jya da yamma a Sakkwato, ya yi fama da rashin lafiya wajen watannin uku, mun yi rashi babba, muna kuma rokon Allah ya gafarta masa ya kuma jikansa da rahma amin. Muna rokon yan uwa su yi masa addu'a koyaushe, ga dan takaitaccen tarihinsa nan a wannan rariyar likau
http:// marubutanhau sa.blogspot. com/2008/ 09/hadi-abdullah i-alkanci. html
Allah ya gafarta masa ya kuma sa mu ma mu cika da imani amin. Dr Yusuf Adamu
Mun samu sakwannin taáziyya da dama, ga kalilan daga cikinsu a kasa:
Ado Ahmad Gidan Dabino
ALLAH AKBAR, Allah ya ji kan Hadi Abdullahi Alkanci. Marubucin Soyayya Ta Fi Kudi (littafin wasan kwaikwayo) da Harsashin Kasa da Shin So Gaskiya Ne? da sauran su. Babu shakka mun yi babban rashi a fagen marubuta, haziki gwarzo a fagen fasaha ya tafi.
Ba zan manta da haduwa ta ta karshe da Hadi ba a lokacin da ya zo Kano wajen bikin kaddamar da littattafan Bashir Othman Tofa, yana cikin mutanen hudu da na yi hira da su a ciki shirin da nake gabatarwa a gidan rediyo FREEDOM mai suna Alkalami Ya Fi Takobi, mutane sun yaba da ire-iren bayanan da ya yi sosai, kuma in yana magana lallai ka san cikakken mutumin Sokoto ne, mai iya karin magana da dabarun zance.Lokacin da na ji labarin rasuwarsa ta hanyar SMS daga Yusuf Adamu ina jihar Lagos, ba shakka na kadu sosai da ganin wannan sakon.
ALLAHU AKBAR! ALLAHU !! AKBAR!!! Allah ka rahamshe shi, ka sa ya huta, mu kuma Allah ya kyauta tamu in ta zo. Allah ka sa gidan Aljanna ce makomarmu baki daya. Amin!!! Ina mika sakon gaisuwa ga dukkanin 'yan'uwa da abokan arziki da dukkan Sakkwatawa.
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJI' UN....Aduk sa'ilin da muka ji wannan kalma tuni take mana nuni da wani gagarumin abu ne ya auku.hakanne yasa nima ina samun wannan rashin jangwarzo mai bada gudunmawa musamman aharkar wasanni, abunda na iya furtawa kenan tare da tawassali da cewa muma tamu tananan zuwa. sai dai muce ubangiji ya kai rahma agareshi. mu kuma Allah yasa mu cika da imani, amin.
*****
Mamane Sahabi Ousmane Alias M.SONiamey Niger
Allahu akbar haka ne, Allah yaji kanshikuma ya sa, ya huta.abida ya bari Allah yabasu hakurida masoya da kuma yan uwa. mu kuma da muka rage in tamu ta zoAllah ya sa, mugama da iskan duniya lafiya Amin.ita rayuwa haka take, kowa lokacin shi, zai jira.ba'a gaggauta wa kowa, kuma ba'a jinkirta wa kowa. kulli nafsi za'ikatil mautko wace rai! sai ta dan-dana mutuwa.gaba dayan mu, muci gaba da yi wa junan mu, addu'a.intamu ta zo, Allah ya sa mucika da kalmar La'ilaha illallah Muhammadu Rasulullah.
******
Sarkin yan Nijar,
Atta Oumaten إنا لله وانا اليه راجعون منهـا خلقناكم وفيهـا وعيدكم ومنهـا نخرجكم تارةاخرى
Dawannan nake meka tsakon ta'aziyar daukacin yan Nijar dake cikin wadannan zauruka, ga iyalai da abokan arziki na wannan ba wan Allah, allah yasa ya huta mu kuma idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani.
***
Uba Dan Zainab
Allah yayimasa rahama yasada shi da annabi sallalahu alaihi wasallamzuriyarsa kuma Allah yashiga lamuransu yasakasu bin surad'al mustaqeem.
****
Ahmad Yahuza Getso (B.A. MIAD, MPPA, HPDCS)
Allah ya gafarta masa ya kyautata tamu.
***
Muhammad Muhammad
Allah ya gafarta masa, mu kuma Allah ya kyauta karshen mu.
***
Isa Muhammad Inuwa
Allah Ya jikan Babban Marubuci Hadi Alkanci, Ya sa mutuwa hutu, Ya kyauta namu zuwan, Ya sa mu je a sa'a. Amin!
****
Muhammad Mansoor
Allah ya sa ya huta amin suma amin.
****
Ibrahim Sheme
Allah Ya jikanshi, ya yi masa rahama. Allahu Akbar! One of the last Titans of Classic Hausa Literature. Wallahi mun yi rashi.
****
Bala Muhammad (A Daidaita Sahu)
Innalillahi Wa inna Ilaihir Raji'un. Allah ya jikansa ya gafarta masa. In tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani, amin.
****
Aisha Zakari
Allah ya jikansa ya gafarta masa, lallai kam mun yi babban rashi.
****
Dr Wale Okediran (ANA President)
May his soul rest in perfect peace, amin.
NASIRU G AHMAD YANAWAKI
A shekarar 1984, ya halarci ajin koyon buga keken rubutu (Typewriting) da ke karkashin Hukumar Yada Ilimin Manya ta Kano, a 1992, ya halarci wani kwas da Jami’ar Musulunci ta Madina ke shiryawa, don horar da malaman Arabiyya da addinin Musulunci, a Jami’ar Bayero ta Kano. A 1992 din dai, ya je wani kwas na addinin Musulunci, a garin Idah, cikin jihar Kogi. A 1999, ya yi wani kwas na karatun gida, karkashin “Sincere Writers Club”, inda ya samu takardar shaida (certificate) kan aikin jarida.
A 1991, ya je jihar “Cross Rivers” inda ya yi aikin jami’i mai duba Malaman Kidaya (Supervisor). Ya koyi sarrafa na’ura mai kwakwalwa a aikace, (Practical) a “Urgent Computers” inda ya taba yin aiki. Yana cikin masu duba wakar Hausa, ta jarrabawar ‘W.A.E.C.’ Wakili ne na jaridar “People And Events”. Editan littattafai ne mai zaman kansa. Ya yi aikin koyarwa a makarantu da dama, (Firamare da Sakandare) tun daga 1984 zuwa yanzu. Yana da sha’awar ziyarce-ziyarce da kulla abota, da karance-karance a kowane fannin ilimi da rayuwa. Ya rubuta litattafai da dama, da wakoki jingim. Nasiru kuma na cikin Sahún gaba na ‘yan Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen jira Kano. A halin yanzu yana karatun digirinsa na biyu a Jamiár Ahmadu Bello (ABU) Zaria.
Monday, June 22, 2009
MUHAMMAD USMAN
HAFSATU AHMAD ABDULWAHID
Sunday, June 14, 2009
BASHIR OTHMAN TOFA
Amarzadan a Birnin Aljanu
Amarzadan da Zoben Farsiyas
Kimiyyar Sararin Samaniya
Tunaninka Kamanninka
Kimiyya da Al'ajaban Al-Qur'ani
Gajerun Labarai
Mu Sha Dariya
Rayuwa Bayan Mutuwa
Saturday, June 13, 2009
UMMA ADAMU
Sakandare a Malam Madori da Sakandaren Kimiyya ta Taura inda ta gama a 1999. Ta ci gaba da karatu daga 2000 a School of Health Technology Jahun da Informatics Institute Kazaure da kuma Jigawa State College of Education har zuwa 2006. A halin yanzu (2009) tana karatu ne a Kano State University of Science and Technology Wudil. Cikin litattafan da ta buga sun hada da:
1. Raino, 2. Rigakafi 3. Sirrinus ko Sirrimu 4. Wahayi 5. Zaman Jira 6. Ya Zalince ni 7. Sabanin Ra'ayi 8. Abu a Duhu.
Tana sha'awar koyarwa da kallon fina-finai da tafiye-tafiye da koyarwa da kuma rubuta kirkirarrun labaru.
Wednesday, May 20, 2009
HIRA DA YARON MALAM
Nine Bajakaden Abubakar Imam. Cewar Yaron Malam. Tun lokaci da shahararren marubucin da a yau duniyar hausawa ke girmamawa a matsayin kakan marubuta ya amsa kira zuwa ga mahaliccinsa, manazarta suka dukufa domin zurfafa nazarin gano ko wanene zai gaji shi marigayin, tare da rike alkalaminsa ga ci gaba da assasa yanayi da kuma salonsa na imamantar da labari zuwa yadda zai dace da Hausawa da kuma al’adunsu. Musamman ma ko domin dinbim amfanin da a yau littattafansa ke dasu ga dalibai sakamakon sanya su da ake yi a manhajar karatu, da kuma zama tushe da suke yi na fara koyon karatu ga mafi yawancin garuruwan Hausawa.
Duk da dai wannan bakin gumurzu ne, wanda sai an samu sadauki mai akwatin siddabaru, ko kuma yakau dan mayakiya da zasu ja tunga, su kuma yi shahada, sannan su fara fafatawa suyi gumu gami da artabu tamkar a tsibirin Bamuda da yahudu badda musumi. Domin ba aiki ne na mata ba, ballantana gimbiya Assadatu ko Bajakadiya ko kuma Mayakiya suyi hargagagin farawa. Amma Abdullahi Mukhtar da ake yiwa lakabi da Yaron Malam, ya sanya sulke tare da daura damarar karbar wannan garkuwa ta Imam kamar yadda ya bayyanawa wakilinmu Maje El-Hajeej Hotoro.
(An yi wannan tattaunawa da shine a watan Janairun 2007)
Zamu fara da jin tarihinka. Sunana Abdullahi Mukhtar Yaron Malam, an kuma haife ni a 1976 a unguwar Fagge dake karamar hukumar Fagge Kano. Na kuma yi karatun firamare na a Fagge Special daga 1984 zuwa 1988. Inda na karasa karatun firamarena a Gama Sabuwa saboda komawa can da muka yi. Dagan nan kuma ban samu damar ci gaba da karatuna ba, sai aka kaini makarantar allo a garin Hadeja. Wacce ban dade ba aka dawo dani, sakamakon rashin lafiya da na yi, inda na ci gaba da karatun allo. Kafin daga baya na shiga makarantar koyom larabci ta Aliyu Bn Abu Thalib, wacce daga baya aka mayar da ita Umar Bn Khattab dake Gyadi-gyadI a nan Kano daga 1994 zuwa 1999. Lokaci guda kuma ina mai ci gaba da halartar karatun azure. Na sake shiga makarantar koyon larabci ta Rasulul Akram, bayan na kamala na tafi Irshadul Umma Islamic College ta Shahuci da ake kira da Aliya daga 2001 zuwa 2004. Wanda a halin yanzu ina jami’ar Bayero, inda nake karanta aikin jarida. Tare da dan hadawa da kasuwanci.
Shin ko a wacce shekara ka fara rubutu, kuma ko menene ya dauki hankalinka har ka shigo fagen?
Alal hakika zan iya cewa tun farko na taso ne da sha’awar rubuce-rubuce, domin tun ina firamare na kan dauki takarda nayi ta kwafar littafin Baba da Inna da kuma Iliya dan mai karfi a cikin littattafan makaranta na. Sannan kuma ni dama makaranci ne na littattafan labaran Larabci da Hausa. Kamar irinsu Magana Jar ice, Yawon Duniyar Haji Baba, Labaran Da da na Yanzu, da sauransu. Domin ko a lokacin da na ke makarantar Allo, ragowar ’yan uwana almajirai kan zagaye ni na rika basu labarin wani littafi dana karanta. Na fara fitar da littafina na farko ne a 1999 wanda na addini ne mai suna Hukunce-hukuncen Azumi da Addu’o’in Watan Ramadan. Sai kuma Hukunce-hukuncen Jinin Haila, amma ban fitar dashi ba, sai bayan da na fitar da littafina mai suna kissoshin Ahlul Baiti. Dagan an kuma sai na fitar da Bajakade da kuma sirrin aure da ma’aurata, wadanda sune litattafan da suka zama sanadiyyar aka anni a duniyar marubuta.
A halin yanzu ko littattafanka sun kai nawa?
Zuwa yanzu na samu nasarar rubuta littattafai da dama kamar, Bajakade, Mayakiya, Bakin gumurzu, Gimbiya Assadatu, Artabu, Fafatawa, Gumu, Tsiburin Bamuda, Sadauki mai akwatin siddabaru, Tunga, Shahada, Bajakadiya, ‘Yar mai ganye, Yakau dan mayakiya da kuma Yahudu badda Musulmi da kuma na addini da dama.
Ko da wane irin salo kake amfani a rubutunka?.
Salon rubutuna sune salon jarumta, abin dariya, soyayya da kuma hikimar Magana. Jigo kuma shine karfafa akidar addinin musulunci, tsayar da adalci da kuma kyautata zamantakewa tsakanin al’ummar musulmi da kuma wadanda ba musulmi ba.
Mafi yawancin irn wadannan littattafai da suke dauke da abubuwan da ka rubuta akan samu fassarowa ake daga wasu littattafai, shin naka ma fassara ne ko kuma kirkirowa kake yi?
Maganar gaskiya ina kirkirar labari na ne, kuma mafi yawanci duk wanda ya dauko wani littafi ya fassara, sai an samu wasu sun daga sun ce ga daga inda ya fassaro. Amma ni babu wanda zai daga littattafaina yace ga daga inda na fassaro. Sai dai ina karance-karance kamar yadda na fada domin kaifafa basirar da Allah Ya yi min, wanda dama ita baiwa ce, amma ilimi, bincike da kuma tambaya akan abin day a shigewa mutum duhu, sune abincin basira. Sannan juya ilimi daga wani harshen zuwa wani ba laifi bane, matukar anyi hakan ta halattacciyar hanya ba satar fasaha ba.
Ko me zaka iya cewa dangane da kalaman Dakta Malumfashi da kuma na Farfesa Abdallah da suka bayyana cewa nan gaba zaka iya gadar Marigayi Abubakar Imam a fagen rubutu?
Wannan ba a bin mamaki bane idan aka yi la’akari da yanayi da kuma salonsa na ban dariya da dabarun zaman duniya da kuma hikimar Magana. Kana kuma yana gina labarin san e akan sigar zamanin da, sannan wani lokaci yak an jefa soyayya. To idan akayi la’akari da yanayin rubuce-rubucena salon da nake bi kenan. Kumai an matukar samun karfafawa akan wannan salon rubutu nawa, domin farfesa Abdallah yak an kira ni da sabon Abubakar Imam. Sannan musamman ya zaunar dani ya bani labarin dabarun da marigayin ke bi a rubutunsa. Sannan akwai Malam B.K Zariya wanda sunyi zamani da Marigayi Imam, shima takanas yakan kirani ya zaunar dani ya sanar dani tarihin yadda rayuwar Abubakar Imam ta kasance, harma yakan kirani da marigayi Imam.
Shin ko akwai wata kyauta da makarantanka suka taba yi maka wacce ba zaka taba mantawa da ita ba?.
Akwai wata a Bauchi da ta taba yi min kyautar Alqur’ani mai girma, wacce a gaskiya bazan manta da wannan kyautar ba. Sannan kuma masoya daga wurare daban-daban, suna yi min fatan alheri wanda wannan ma babbar kyauta ce, dab a zan manta da ita ba.
Ko a wane irin yanayi ka fi son yin rubutu?
Ina yin rubutu a kowane irin yanayi, amma nafi jin dadin yanayin bayan sallar asuba. Amma a yanzu na dauki wani salo nana yin rubutu a bakin ruwa, ko cikin daji mai bishiyu da kuma ciyayi, ko wajen gari kamar yadda Abubakar Imam ya yi.
Ko shin a matsayinka na dan kasuwa yaya kake hada harkar rubutu da kuma kasuwanci lokaci guda?.
Ai shi rubutu baya hana marubuci yi wasu abubuwan yau da kullum. Misali idan ka dauki marigayi Imam malamin malakaranta ne kuma marubuci lokaci guda. Sannan daga bisani ya zama Editan wata jarida, wanda a wannan lokacin babban aiki ne saboda karancin kayan aiki. Haka ma a yau zaka samu marubuta suna kuma wasu abubuwa na daban, ciki hard a sojoji da ‘yan sanda da sauran ayyukan gwamnati ko kuma na kamfani kuma wannan baya hana su rubutu.
Da kayi maganar kasuwanci sai ka tuno da korafin da wasu marubuta ke yi na matsalar ‘yan kasuwa, wajen rashin sakar musu kudadensu da wuri bayan an sayar da kayansu.?
Lallai kam wannan matsala ce da muka dade muna kuka da ita, amma yanzu alhamduLillahi al’amura sun fara kyautata, domin zaka samu mud a kanmu marubutan muna yabon wasu ‘yan kasuwar da kokarin bayar da kudI akan kari. Su kuma wadanda ake samun jinkirin sun dauki alwashin magance hakan. Sannan kuma kungiyar masu littattafai da kuma ‘yan kasuwa, suna aiki tukuru wajen ganin ta magance wannan matsala. Mu kara hakuri nan ba jimawa ba, komai zai zama tarihi Insha Allahu.
Kwanakin baya kungiyar marubuta ta kasa reshen jihar Kano (ANA) ta jagoranci marubutan Hausa wata tafiya zuwa kasar Nijar. Kasancewar kana cikin shugabannin wannan kungiya, ko wadanne matsaloli da kuma nasarori kuka samu yayin wannan tafiya.?
Makasudin wannan tafiya shine ziyara da kuma taron karawa juna sani tsakanin marubutan Nijeriya da kuma na waccan kasa. Kana kuma da yin bincike akan yanayin zamantakewa da al’adunsu domin samun karin gogewa ga marubutanmu na nan. Matsala kadai da muka samu ita ce ta motarmu da ta lalace, wanda hakan ya tilasta mana yin amfani da guzurinmu domin kara hayar wata motar da ta karasa dam u can. Mun kuma samu nasarori sosai musamman ma na karawa juna sani, sannan ga kuma ziyarar muhimman wurare da muka yi, sun kuma karrama mu sosai domin hidimomi da suka yi man na tsaro da kuma makwanci. Sannan kuma mun fa’idantu matuka gaya , basirarmu ta kara fadada, wanda dama masu hikima sunce tafiya mabudin ilimi.
TA'AZIYYAR YARON MALAM
Dr Yusuf M Adamu
Shugaban ANA Kano
Dannan wannan rariyar likau don karanta takaitaccen tarihin Abdullahi Muktar Yaron Malam: http://marubutanhausa.blogspot.com/2009/02/abdullahi-mukhtar-yaron-malam.html
Saturday, May 2, 2009
KABIRU YUSUF ANKA
Sunday, February 22, 2009
ABDULLAHI MUKHTAR (YARON MALAM)
Friday, February 20, 2009
ZAHARADDEEN IBRAHIM KALLAH

Friday, December 5, 2008
AISHA ZAKARI

Aisha Zakari 'yar asalin Hadejia, fitacciyar marubuciya ce, kodayake ta fi karfi a rubutun turanci daga baya ta fara rubutun Hausa. Ta samu digirinta na farko a fanning Labarin Kasa (Geography) daga Jamiár Bayero ta Kano kuma tana cikin wadanda suka rubuta wani wasan kwaikwayo na gidan Radiyon BBC watau Gatanan Gatananku ta kuma rubuta waken turanci da dama wadanda aka buga a litattafai da kuma gidajen yana. Ta taba zama Magatakardar Kudi ta Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) ta Kasa kuma ta rike mukamai a ANA Kano da dama hard a na Mataimakiyar Shugaba. Aisha Fellow ce ta Leadership Development Mechanism (LDM Fellow) kuma tana daya daga cikin hazikan matasa da suka taimakawa adabin Hausawa da Hausawa kuma a halin yanzu tana zaune da mijinta a Amurka inda take ci gaba da karatu.
Littafinta da ta rubuta ko ta fito a ciki sun hada da:
Himma Ba Ta Ga Raggo
Verses in Absentia Poetry of Aisha Usman Bugaje (Coeditor)
Pregnant Skies: Anthology of 50 Nigerian Poets
Mazan Fara: ANA Zamfara Anthology of Poems and Short Stories
Tuesday, October 7, 2008
NURA ADO GEZAWA

Nuraddeen ya fara daukar biro ya dora a kan takarda da sunan rubuta littafi a shekarar 1994, kuma littafin farko da ya fara hattama rubutawa shine AN YI TSALLEN... amma littafin da ya fara fitarwa shine RUMBUN TUNANI. Nuraddeen ya yi rubuce-rubucen kirkirarrun labarai da dama, daga cikin su akwai BAKIN RIJIYA wanda ma'aikatar ilimi ta K.E.R.D ta tace a takarda mai taken K.E.R.D/PROP/22/T/V.I/31, tacewar da ta yi sanadiyyar sayen littafin da ma'aikatar ilimi, da ma'aikatar ilimin firamare suka saya.
Kirkirarrun littafan da Nuraddeen ya rubuta sun hadar da;
Rumbun Tunani, Ba Zama, Bakin Rijiya, Laifi Inuwa, Tokar Danasani, An Yi Tsallen, Rai Dangin Goro (Taskata) Gyara Kayanka, Tsaftataccen Mahaukaci, Ba shiga JIrgin Ba, Ramin Kura, da kuma Abu Kamar Wasa.
Haka nan kasancewar Nuraddeen cikakken dan kungiyar ANA reshen jihar Kano, ya gabatar da gajerun labarai a taron ANA da ake yi duk watan duniya, wasu daga ciki sun hadar da; BAKIN DARE, KOWANE GAUTA, UNGULU DA KAN ZABUWA, SAI DA RUWAN CIKI.., SAGAU, GARIN NEMAN GIRA, DA SIRADIN RUBUTU.
Dadin dadawa, Nuraddeen ya yi wakoki da suka hadar da Rubdugu, Kyawun hali, Shugaban Kowa, Kin wanda Ya Rasa da Tarnakin Bakar Rayuwa.
A fagen addinin Musulunci, Nuraddeen ya rubuta littafai kamar haka; Sabani A Duniyar Musulunci da kuma Rudanin Rayuwa Da Musulunci.
Nuraddeen, har ila yau, ya yi rubutun gajerun labaran turanci da suka zama cikin shafuffukan yanar gizon Helium, wadanda suka hadar da My True Colours, The World of Hate, Brave Or Coward?
A halin yanzu Nuraddeen yana daf da komawa don karasa karatun digirinsa na farko. kuma bai yi aure ba ballantana a je ga batun iyali. Babban abin da ya ke burgeshi shine kokarin da aka yi don kyautata rayuwar da tarnakin rayuwa ya cukwikwiye.
Za a iya tuntubar da Nuraddeen Gezawa ta wadannan hanyoyi;
salmannhur@yahoo.com, 07028821493, 08077879218.
Sunday, September 28, 2008
ZAKARIYA MUHAMMAD SARKI

Zakariyya ya taba aikin kamfani a Kano da Legas a tsakanin shekarun 1995 zuwa 1999. Aikin da ya yi a Legas ya ba shi damar yin rubuce-rubuce a wasu fitattun jaridu na Kudancin Nijeriya kamar ‘The Punch’, ‘The Post Express’ da dai sauran irinsu. Haka kuma Zakariyya ya taba zama babban wakili (Bureau Chief) na Legas na kamfanin jaridar ‘The Shield Weekly’ da kuma Garkuwa da ke Kano. Ya taba zama wakilin Mujallar Fim a Kano. Hakanan kuma Marubuci na Musamman ga tsohuwar Mujallar ‘Mumtaz’ ta shahararren marubucin nan Ado Ahmad Gidan Dabino.
Zakariyya ya rubuta littattafai da kuma wakoki kirkirarru masu dama sai dai kuma ba’a taba buga ko daya daga ciki ba saboda wani shiri da yake da shi nan gaba (a shekarar 2009). Duk da haka a shekarar 2005 an juya littafinsa mai suna “Wuta a Masaka” zuwa fim mai taken “Wahami”, wanda darakta Ado Gidan Dabino ya bada Umarni. Zakariyya memba ne na Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen Jihar Kano. Ya na da mata da ya’ya biyu, kuma yanzu yana zaune a Kano.
Za a iya ziyartar blog din shi mai adireshi kamar haka http://www.zakariyyasarki.blogspot.com/
Ko kuma adireshin email : zakariyyasarki2005@yahoo.co.uk, zakariyyasarki@ymail.com
Lambobin Waya : 080-24388438, 064-893104, 064-317582.

