Monday, June 22, 2009

MUHAMMAD USMAN


Muhammad Usman wanda kuma aka sani da Sunusi Shehu Daneji na daya daga cikin turakun da su assassan adabin Hausa na zamani. Marubuci, mai dab'i kuma mai wallafa mujallar Hausa. Marubuci ne wanda ya ci gaba da bada jagora ga marubutan Hausa na zamani tare da kokarin samar da adabi mai tarbiyya. Yana rubuce-rubuce na tarbiyya da kimiyyar sararin samaniya da sauransu. Cikin litattafansa akwai:

Bankwana da Masoyi

Yaron Kirki

Madubin Imani

HAFSATU AHMAD ABDULWAHID


An haifi Hajiya Hafsatu a Birnin Kano. Ta yi karatunta na boko a Kano kafin ta yi aure ta koma Gusau da zama. Fitacciyar marubuciyar Hausa ce wadda littafinta na So Aljannar Duniya shi ne littafin zube na farko da mace ta rubuta a harshen Hausa. Ta wallafa 'Yardubu Mai Tambotsai da kuma Saba Dan Sababi. Tana kuma rubutu da turanci da kuma fillanci. Marubuciya ce wadda ke da kishin rubutu ta kan kuma halarci tarurrukan marubutan Hausa da na Nijeriya. Bayan rubutu takan taba siyasa don ta taba takarar Gwamna a jihar Zamfara.

Sunday, June 14, 2009

BASHIR OTHMAN TOFA



Fitaccen dan siyasa kuma hamshakin dan kasuwa wanda kuma ya yanke shawarar yin amfani da basirar da Allah ya yi masa ya zama marubuci. Bashir Tofa ya yi rubuce-rubuce da harshen Hausa bisa zabin ciyar da harshen gaba. Ya wallafa litattafan Hausa da dama wadanda suka hada da na kirkira da kuma na ilmi. Cikin litattafansa da suka fito sun hada da:

Amarzadan a Birnin Aljanu
Amarzadan da Zoben Farsiyas
Kimiyyar Sararin Samaniya
Tunaninka Kamanninka
Kimiyya da Al'ajaban Al-Qur'ani
Gajerun Labarai
Mu Sha Dariya
Rayuwa Bayan Mutuwa

Saturday, June 13, 2009

BINTA RABIÚ SIPIKIN



(Za mu kawo bayanai a kanta bada jimawa ba)

UMMA SULAIMAN 'YAN AWAKI


Fitacciyar marubuciyar Hausa Umma Sulaiman 'Yan Awaki... (za mu kawo bayanan nan gaba kadan)

UMMA ADAMU


An haifi Umma Adamu ranar 15th ga Oktoba 1981 a Gwarzo, duk da cewa ita 'yar asalin Hadejia ce. Ta yi karatun Firamare a Kanti Primary School Kazaure daga 1987-2003. Ta kuma yi karatun

Sakandare a Malam Madori da Sakandaren Kimiyya ta Taura inda ta gama a 1999. Ta ci gaba da karatu daga 2000 a School of Health Technology Jahun da Informatics Institute Kazaure da kuma Jigawa State College of Education har zuwa 2006. A halin yanzu (2009) tana karatu ne a Kano State University of Science and Technology Wudil. Cikin litattafan da ta buga sun hada da:

1. Raino, 2. Rigakafi 3. Sirrinus ko Sirrimu 4. Wahayi 5. Zaman Jira 6. Ya Zalince ni 7. Sabanin Ra'ayi 8. Abu a Duhu.

Tana sha'awar koyarwa da kallon fina-finai da tafiye-tafiye da koyarwa da kuma rubuta kirkirarrun labaru.

Wednesday, May 20, 2009

HIRA DA YARON MALAM

Daga Maje El-Hajeej <sirrinsu@yahoo. com>


Nine Bajakaden Abubakar Imam. Cewar Yaron Malam. Tun lokaci da shahararren marubucin da a yau duniyar hausawa ke girmamawa a matsayin kakan marubuta ya amsa kira zuwa ga mahaliccinsa, manazarta suka dukufa domin zurfafa nazarin gano ko wanene zai gaji shi marigayin, tare da rike alkalaminsa ga ci gaba da assasa yanayi da kuma salonsa na imamantar da labari zuwa yadda zai dace da Hausawa da kuma al’adunsu. Musamman ma ko domin dinbim amfanin da a yau littattafansa ke dasu ga dalibai sakamakon sanya su da ake yi a manhajar karatu, da kuma zama tushe da suke yi na fara koyon karatu ga mafi yawancin garuruwan Hausawa.

Duk da dai wannan bakin gumurzu ne, wanda sai an samu sadauki mai akwatin siddabaru, ko kuma yakau dan mayakiya da zasu ja tunga, su kuma yi shahada, sannan su fara fafatawa suyi gumu gami da artabu tamkar a tsibirin Bamuda da yahudu badda musumi. Domin ba aiki ne na mata ba, ballantana gimbiya Assadatu ko Bajakadiya ko kuma Mayakiya suyi hargagagin farawa. Amma Abdullahi Mukhtar da ake yiwa lakabi da Yaron Malam, ya sanya sulke tare da daura damarar karbar wannan garkuwa ta Imam kamar yadda ya bayyanawa wakilinmu Maje El-Hajeej Hotoro.

(An yi wannan tattaunawa da shine a watan Janairun 2007)

Zamu fara da jin tarihinka. Sunana Abdullahi Mukhtar Yaron Malam, an kuma haife ni a 1976 a unguwar Fagge dake karamar hukumar Fagge Kano. Na kuma yi karatun firamare na a Fagge Special daga 1984 zuwa 1988. Inda na karasa karatun firamarena a Gama Sabuwa saboda komawa can da muka yi. Dagan nan kuma ban samu damar ci gaba da karatuna ba, sai aka kaini makarantar allo a garin Hadeja. Wacce ban dade ba aka dawo dani, sakamakon rashin lafiya da na yi, inda na ci gaba da karatun allo. Kafin daga baya na shiga makarantar koyom larabci ta Aliyu Bn Abu Thalib, wacce daga baya aka mayar da ita Umar Bn Khattab dake Gyadi-gyadI a nan Kano daga 1994 zuwa 1999. Lokaci guda kuma ina mai ci gaba da halartar karatun azure. Na sake shiga makarantar koyon larabci ta Rasulul Akram, bayan na kamala na tafi Irshadul Umma Islamic College ta Shahuci da ake kira da Aliya daga 2001 zuwa 2004. Wanda a halin yanzu ina jami’ar Bayero, inda nake karanta aikin jarida. Tare da dan hadawa da kasuwanci.

Shin ko a wacce shekara ka fara rubutu, kuma ko menene ya dauki hankalinka har ka shigo fagen?
Alal hakika zan iya cewa tun farko na taso ne da sha’awar rubuce-rubuce, domin tun ina firamare na kan dauki takarda nayi ta kwafar littafin Baba da Inna da kuma Iliya dan mai karfi a cikin littattafan makaranta na. Sannan kuma ni dama makaranci ne na littattafan labaran Larabci da Hausa. Kamar irinsu Magana Jar ice, Yawon Duniyar Haji Baba, Labaran Da da na Yanzu, da sauransu. Domin ko a lokacin da na ke makarantar Allo, ragowar ’yan uwana almajirai kan zagaye ni na rika basu labarin wani littafi dana karanta. Na fara fitar da littafina na farko ne a 1999 wanda na addini ne mai suna Hukunce-hukuncen Azumi da Addu’o’in Watan Ramadan. Sai kuma Hukunce-hukuncen Jinin Haila, amma ban fitar dashi ba, sai bayan da na fitar da littafina mai suna kissoshin Ahlul Baiti. Dagan an kuma sai na fitar da Bajakade da kuma sirrin aure da ma’aurata, wadanda sune litattafan da suka zama sanadiyyar aka anni a duniyar marubuta.

A halin yanzu ko littattafanka sun kai nawa?
Zuwa yanzu na samu nasarar rubuta littattafai da dama kamar, Bajakade, Mayakiya, Bakin gumurzu, Gimbiya Assadatu, Artabu, Fafatawa, Gumu, Tsiburin Bamuda, Sadauki mai akwatin siddabaru, Tunga, Shahada, Bajakadiya, ‘Yar mai ganye, Yakau dan mayakiya da kuma Yahudu badda Musulmi da kuma na addini da dama.

Ko da wane irin salo kake amfani a rubutunka?.
Salon rubutuna sune salon jarumta, abin dariya, soyayya da kuma hikimar Magana. Jigo kuma shine karfafa akidar addinin musulunci, tsayar da adalci da kuma kyautata zamantakewa tsakanin al’ummar musulmi da kuma wadanda ba musulmi ba.

Mafi yawancin irn wadannan littattafai da suke dauke da abubuwan da ka rubuta akan samu fassarowa ake daga wasu littattafai, shin naka ma fassara ne ko kuma kirkirowa kake yi?
Maganar gaskiya ina kirkirar labari na ne, kuma mafi yawanci duk wanda ya dauko wani littafi ya fassara, sai an samu wasu sun daga sun ce ga daga inda ya fassaro. Amma ni babu wanda zai daga littattafaina yace ga daga inda na fassaro. Sai dai ina karance-karance kamar yadda na fada domin kaifafa basirar da Allah Ya yi min, wanda dama ita baiwa ce, amma ilimi, bincike da kuma tambaya akan abin day a shigewa mutum duhu, sune abincin basira. Sannan juya ilimi daga wani harshen zuwa wani ba laifi bane, matukar anyi hakan ta halattacciyar hanya ba satar fasaha ba.

Ko me zaka iya cewa dangane da kalaman Dakta Malumfashi da kuma na Farfesa Abdallah da suka bayyana cewa nan gaba zaka iya gadar Marigayi Abubakar Imam a fagen rubutu?
Wannan ba a bin mamaki bane idan aka yi la’akari da yanayi da kuma salonsa na ban dariya da dabarun zaman duniya da kuma hikimar Magana. Kana kuma yana gina labarin san e akan sigar zamanin da, sannan wani lokaci yak an jefa soyayya. To idan akayi la’akari da yanayin rubuce-rubucena salon da nake bi kenan. Kumai an matukar samun karfafawa akan wannan salon rubutu nawa, domin farfesa Abdallah yak an kira ni da sabon Abubakar Imam. Sannan musamman ya zaunar dani ya bani labarin dabarun da marigayin ke bi a rubutunsa. Sannan akwai Malam B.K Zariya wanda sunyi zamani da Marigayi Imam, shima takanas yakan kirani ya zaunar dani ya sanar dani tarihin yadda rayuwar Abubakar Imam ta kasance, harma yakan kirani da marigayi Imam.

Shin ko akwai wata kyauta da makarantanka suka taba yi maka wacce ba zaka taba mantawa da ita ba?.
Akwai wata a Bauchi da ta taba yi min kyautar Alqur’ani mai girma, wacce a gaskiya bazan manta da wannan kyautar ba. Sannan kuma masoya daga wurare daban-daban, suna yi min fatan alheri wanda wannan ma babbar kyauta ce, dab a zan manta da ita ba.

Ko a wane irin yanayi ka fi son yin rubutu?
Ina yin rubutu a kowane irin yanayi, amma nafi jin dadin yanayin bayan sallar asuba. Amma a yanzu na dauki wani salo nana yin rubutu a bakin ruwa, ko cikin daji mai bishiyu da kuma ciyayi, ko wajen gari kamar yadda Abubakar Imam ya yi.

Ko shin a matsayinka na dan kasuwa yaya kake hada harkar rubutu da kuma kasuwanci lokaci guda?.
Ai shi rubutu baya hana marubuci yi wasu abubuwan yau da kullum. Misali idan ka dauki marigayi Imam malamin malakaranta ne kuma marubuci lokaci guda. Sannan daga bisani ya zama Editan wata jarida, wanda a wannan lokacin babban aiki ne saboda karancin kayan aiki. Haka ma a yau zaka samu marubuta suna kuma wasu abubuwa na daban, ciki hard a sojoji da ‘yan sanda da sauran ayyukan gwamnati ko kuma na kamfani kuma wannan baya hana su rubutu.

Da kayi maganar kasuwanci sai ka tuno da korafin da wasu marubuta ke yi na matsalar ‘yan kasuwa, wajen rashin sakar musu kudadensu da wuri bayan an sayar da kayansu.?
Lallai kam wannan matsala ce da muka dade muna kuka da ita, amma yanzu alhamduLillahi al’amura sun fara kyautata, domin zaka samu mud a kanmu marubutan muna yabon wasu ‘yan kasuwar da kokarin bayar da kudI akan kari. Su kuma wadanda ake samun jinkirin sun dauki alwashin magance hakan. Sannan kuma kungiyar masu littattafai da kuma ‘yan kasuwa, suna aiki tukuru wajen ganin ta magance wannan matsala. Mu kara hakuri nan ba jimawa ba, komai zai zama tarihi Insha Allahu.

Kwanakin baya kungiyar marubuta ta kasa reshen jihar Kano (ANA) ta jagoranci marubutan Hausa wata tafiya zuwa kasar Nijar. Kasancewar kana cikin shugabannin wannan kungiya, ko wadanne matsaloli da kuma nasarori kuka samu yayin wannan tafiya.?
Makasudin wannan tafiya shine ziyara da kuma taron karawa juna sani tsakanin marubutan Nijeriya da kuma na waccan kasa. Kana kuma da yin bincike akan yanayin zamantakewa da al’adunsu domin samun karin gogewa ga marubutanmu na nan. Matsala kadai da muka samu ita ce ta motarmu da ta lalace, wanda hakan ya tilasta mana yin amfani da guzurinmu domin kara hayar wata motar da ta karasa dam u can. Mun kuma samu nasarori sosai musamman ma na karawa juna sani, sannan ga kuma ziyarar muhimman wurare da muka yi, sun kuma karrama mu sosai domin hidimomi da suka yi man na tsaro da kuma makwanci. Sannan kuma mun fa’idantu matuka gaya , basirarmu ta kara fadada, wanda dama masu hikima sunce tafiya mabudin ilimi.

TA'AZIYYAR YARON MALAM

Allah ya yi wa Abdullahi Muktar Yaron Malam rasuwa ranar Lahadi 17 ga Mayu 2009 da misalin sha biyu na rana, a dakin Karatu na Muratala Muhammad dake birnin Kano. Ya rasu ya bar mata daya da diya uku. Fitaccen marubuci, shugaban Brigade Authors Forum (BAF) kuma jami'i a Kungiyar Marubuta ta Nigeria (ANA) reshen Jihar Kano, Yaron Malam marubuci ne ingarma wanda ya bada muhimmiyar gudunmuwa wurin ci gaban adabin Hausa. Yaron Malam kuma mawallafi ne kuma mai sayar da littattafai. Mun yi babban rashi. Allah ya jikan Yaron Malam ya gafarta masa amin.


Dr Yusuf M Adamu
Shugaban ANA Kano

Dannan wannan rariyar likau don karanta takaitaccen tarihin Abdullahi Muktar Yaron Malam: http://marubutanhausa.blogspot.com/2009/02/abdullahi-mukhtar-yaron-malam.html

Saturday, May 2, 2009

KABIRU YUSUF ANKA



An haifi Kabiru Yusuf Fagge (anka), a unguwar Fagge. Ya fara karatun Alkur'ani a makarantun allo, da Islamiyya ta Sabilul Rashad da ke Gyadi-gyadi da Mukhtariyya Islamiyya da ke unguwar Fagge da kuma Thimarul Kur'an (bangaren dare) ya sami saukar Kur'ani, da karanta sauran littattafan addini.
Ya fara karatun Firamare a Kurna Special Primary School da sakandire a JSS Kurna,  Sai Jami'ar Bayero inda ya sami shaidar Diploma a bangaren aikin jarida (Mass Communication), sannan kuma ya samu shaidar karatun Diploma a bangaren Statistics, da kuma Diploma a na'ura mai kwakwalwa (Computer) a makarantun: Online Computer da kuma Hands-On Computer Institute inda ya karanci (Desktop Publishing da Data Processing and Maintenance), ya karanci Diploma in Film and Television Production a Northwest University, Kano, a wannan shekara ta 2020 yana Jami'ar Bayero, yana karantar Hausa.
Ya sami kwarewa a fannin sarrafa na'ura mai kwakwalwa musamman a bangaren zane da bugu (design graphics and typing).
Ya buga littattafai, jaridu da mujallu masu yawa a bugun kwamfiyuta, ya kuma tsara shafukan mujallu da jaridu da kuma tsara bangwayen littattafai da yawa.
Ya yi rubuce-rubuce a jaridu da mujallu  kamar haka:-
Wakiliya -(mujallar Marubuta) - a matsayin mataimakin Edita.
Inuwar Marubuta -(mujallar Marubuta) - marubuci na musamman
Suda -(mujallar 'yan fim) - marubuci
Kwallon Kafa -(mujallar labarun wasanni) -mataimakin Edita.
Muryar 'Yanci -(jaridar labaran karamar hukumar Fagge) -Edita
Masoya -(mujallar labaran rayuwa da soyayya) - Edita
Kakaki -(mujallar kare ra'ayin karamar hukumar Fagge) -Edita
Haka ya yi rubuce-rubuce da dama a jaridu da mujallu na kasar nan. Ya wallafa littattafai da dama.

YADDA YA SAMI KANSA A RUBUCE-RUBUCE
Tun a aji hudu na firamare ya zama mai iya karance-karancen littattafan Hausa da Jaridu, shi da wani abokin karatu mai suna Abdulhamid Muhammad Al'ansari wanda asalinsa Kwara ne, da shi suke siyo littattafan da jaridu suna karantawa, don haka sai ya fara karanta MAGANA JARI CE a ajinsu, daga nan ya sami kan sa a rubuce-rubuce.
LITTAFAN DA YA RUBUTA
Ya rubuta littattafai da dama, amma wadanda ya fitar guda goma bangaren hikaya:
1. Karfin Hali
2. Shure-shure
3. Ninkaya
4. Alwashi
5. Bilkisu
6. Firgita Samari...
7. Rayya
8. 'Yanmata
9. Kushewar Badi
10. Launin So

Sai kuma littattafan ilimi na koyarwa
The Boy Who Cried Wolf (anthology of short stories)
Dabarun Rubuta Kagaggun Labarai
Mu Koyi Karatu 1,2,3,4,5
Tatsuniyoyi Da Labarun Gargajiya

Sai kuma littafan WASAN KWAIKWAYO:
1. KOWA YA YI DA KYAU
2. TUTAR BABU
3. KURMAN AMO

Sai kuma littattafan da suka shafi bandariya da sauran hikaya
1. Mu Sha Dariya
2. Kai Ma Ka Dara
3. Abokin Dariya
4. Malamin Ban Dariya
5. A Ba Su Dariya
6. Gidan Dariya
7. Zunbuli Kakan Marowata

Sannan akwai littattafan da suka shafi koyar da yara kanana karatu da rubutu kamar:
1. Standard Dictionary
2. The Boy Who Cried Wolf
3. Alphabet for Kids
4. Mathematics for Kids
5. Successful Drawing Book for Children
Da sauransu

FINA-FINAI
Ninkaya, 
Sulusi, 
Sakin Aure, 
Hakkin Miji, 
Aure Ibada Ne, 
Sallamar Bankwana, 
Sharri Kayan Kwalba, 
Karshenki, 
Matar Waye?, 
Mahaifiyarmu, 
Wa Ya Kasheta?, 
Dan Garba, 
Sarkin Barayi, 
Sarkin Aska, 
Kwalba
Wace Ce Ni?
Goyon Kaka

Series
'Ya'yanmu, 
Mu Sha Dariya, 
Butulcin Zuci


Yana da aure da 'ya'ya

Sunday, February 22, 2009

ABDULLAHI MUKHTAR (YARON MALAM)


An haife shi ranar 1/6/76 a unguwar Fagge. Ya yi makarantar Fagge Special Primary School Ibrahim Taiwo Road. Daga nan suka koma Birged da zama inda ya karasa firamare a Birged Special primary School. Ya shiga Aliyu Bn Abu Talib School daga 1991-1996. Daga nan ya koma makarantar zaure don ci gaba da karatun addini zuwa 2005. A 2005 ne ya yi karatun Professional Diploma a BUK.
Litattafansa na Hausa sun hada da:
Bajakade
Mayakiya
Bakin Gumurzu
Gimbiya Assadatu
Artabu
Gumu
Tunga
Bajakadiya'(Ýar Mai ganye)
Sihirtacciya
Yahudu Badda Musulmi
Tsibirin Bamuda
Yakau
Sirrin Aure da Maáurata A Muslunci
Duniyar Maáurata A Muslunci
Ku Tambayeni Kafin Ku Rasa Ni
Kuriá
Hukunce-Hukuncen Jinin Haila
Hassada da Maganinta A Muslunci
Kissoshin Ahlul Baiti

Friday, February 20, 2009

ZAHARADDEEN IBRAHIM KALLAH


Zaharaddeen Ibrahim Kallah ya yi digirinsa a kan ilimin zamantakewar dan Adam da kuma siyasa. Marubuci ne da yake rubutu a harsuna guda biyu, hausa da turanci. Ya taba lashe gasar rubutun waka ta turanci ta duniya a shekara ta 2004, da Negerian.Biz suka shirya. Yana daga cikin shugabanni gudanarwa na ANA. A hali yanzu yana aiki da Strategic Planning a Jami’ar Bayero ta Kano. Ya rubuta littafin Karkon Dabino sannan ya fito a littafai na gamayya da suka hada da Five hundred Nigerian poets, da Mazan Fara. Littafansa da suke hanyar fitowa sun hada da So ko Wahala da Usman Mai duniya da Lokaci Bako ne da Love in Mayuwandu tare da The Right Choice.

Friday, December 5, 2008

AISHA ZAKARI




Aisha Zakari 'yar asalin Hadejia, fitacciyar marubuciya ce, kodayake ta fi karfi a rubutun turanci daga baya ta fara rubutun Hausa. Ta samu digirinta na farko a fanning Labarin Kasa (Geography) daga Jamiár Bayero ta Kano kuma tana cikin wadanda suka rubuta wani wasan kwaikwayo na gidan Radiyon BBC watau Gatanan Gatananku ta kuma rubuta waken turanci da dama wadanda aka buga a litattafai da kuma gidajen yana. Ta taba zama Magatakardar Kudi ta Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) ta Kasa kuma ta rike mukamai a ANA Kano da dama hard a na Mataimakiyar Shugaba. Aisha Fellow ce ta Leadership Development Mechanism (LDM Fellow) kuma tana daya daga cikin hazikan matasa da suka taimakawa adabin Hausawa da Hausawa kuma a halin yanzu tana zaune da mijinta a Amurka inda take ci gaba da karatu.
Littafinta da ta rubuta ko ta fito a ciki sun hada da:
Himma Ba Ta Ga Raggo
Verses in Absentia Poetry of Aisha Usman Bugaje (Coeditor)
Pregnant Skies: Anthology of 50 Nigerian Poets
Mazan Fara: ANA Zamfara Anthology of Poems and Short Stories

Tuesday, October 7, 2008

NURA ADO GEZAWA


An haifi Nuraddeen Gezawa (SALMAN NHUR) a ranar lahdi shabiyu ga watan janairun shekarar 1980 miladiyya, wadda ta zo daidai da ashirin da hudu ga watan safar na shekarar 1400 hijiriyya. An haife shi ne cikin garin Gezawa na karamar hukumar Gezawa ta jihar Kano a tarayyar Najeriya. Ya fara karatunsa na muhammadiyya da na boko (firamare da karamar sakandare) a cikin garin na Gezawa, daga shekarar 1986 zuwa 1994. Daga nan sai ya cigaba da karatunsa na babbar sakandare a makarantar kimiyya ta Dawakin Tofa daga shekarar 1994 zuwa 1997. Nuraddeen ya yi aiki da bangaren lafiya na sakatariyar karamar hukumar Gezawa, inda ya koma karatunsa na share fagen shiga Jami'a a C.A.S ta Kano, a shekara ta 2000. Daga nan sai Nuraddeen ya zarce zuwa Jami'ar Usmanu Danfodiyo dake Sokoto a shekara ta 2001. Ko da yake dai hikima ta Ubangiji ta sanya bai samu damar ko da cin karfin karatun a Jami'ar ta Sokoto ba, saboda matsalolin da suka tilasta masa daukar hutun dole.

Nuraddeen ya fara daukar biro ya dora a kan takarda da sunan rubuta littafi a shekarar 1994, kuma littafin farko da ya fara hattama rubutawa shine AN YI TSALLEN... amma littafin da ya fara fitarwa shine RUMBUN TUNANI. Nuraddeen ya yi rubuce-rubucen kirkirarrun labarai da dama, daga cikin su akwai BAKIN RIJIYA wanda ma'aikatar ilimi ta K.E.R.D ta tace a takarda mai taken K.E.R.D/PROP/22/T/V.I/31, tacewar da ta yi sanadiyyar sayen littafin da ma'aikatar ilimi, da ma'aikatar ilimin firamare suka saya.

Kirkirarrun littafan da Nuraddeen ya rubuta sun hadar da;
Rumbun Tunani, Ba Zama, Bakin Rijiya, Laifi Inuwa, Tokar Danasani, An Yi Tsallen, Rai Dangin Goro (Taskata) Gyara Kayanka, Tsaftataccen Mahaukaci, Ba shiga JIrgin Ba, Ramin Kura, da kuma Abu Kamar Wasa.

Haka nan kasancewar Nuraddeen cikakken dan kungiyar ANA reshen jihar Kano, ya gabatar da gajerun labarai a taron ANA da ake yi duk watan duniya, wasu daga ciki sun hadar da; BAKIN DARE, KOWANE GAUTA, UNGULU DA KAN ZABUWA, SAI DA RUWAN CIKI.., SAGAU, GARIN NEMAN GIRA, DA SIRADIN RUBUTU.

Dadin dadawa, Nuraddeen ya yi wakoki da suka hadar da Rubdugu, Kyawun hali, Shugaban Kowa, Kin wanda Ya Rasa da Tarnakin Bakar Rayuwa.

A fagen addinin Musulunci, Nuraddeen ya rubuta littafai kamar haka; Sabani A Duniyar Musulunci da kuma Rudanin Rayuwa Da Musulunci.

Nuraddeen, har ila yau, ya yi rubutun gajerun labaran turanci da suka zama cikin shafuffukan yanar gizon Helium, wadanda suka hadar da My True Colours, The World of Hate, Brave Or Coward?

A halin yanzu Nuraddeen yana daf da komawa don karasa karatun digirinsa na farko. kuma bai yi aure ba ballantana a je ga batun iyali. Babban abin da ya ke burgeshi shine kokarin da aka yi don kyautata rayuwar da tarnakin rayuwa ya cukwikwiye.
Za a iya tuntubar da Nuraddeen Gezawa ta wadannan hanyoyi;
salmannhur@yahoo.com, 07028821493, 08077879218.

Sunday, September 28, 2008

BARKA DA SALLAH

Da fatan kowa ya yi sallah lafiya. Allah ya ba mu ladan azumi ya kuma maimaita mana mu ga ta badin badadadadada... amin summa amin.

ZAKARIYA MUHAMMAD SARKI


An haifi Zakariyya Muhammad Sarki, a garin Kazaure ta Jihar Jigawa a shekarar 1976. Bayan karatun Muhammadiya, ya yi karatun Firamare da na karamar Sikandire a Kudu Central Primary da kuma Sikandiren Gwamnati da ke Kazaure a in da ya kamala a shekarar 1991. A lokacin ne kuma sha’awar rubuce-rubuce da karance-karance musamman na marubuta hausawa ya fara shiga zuciyarsa. Wannan ya sa ya zama mafi iya karatun littafi a cikin yan’uwansa dalibai. Duk da dai ba zai iya tuna labari daya da ya taba rubutawa ba a wancan lokaci, ya ‘saukewa’ yan ajinsu na firamare da na sikandire littatafai na Hausa irin su Magana Jari Ce, Iliya Dan Maikarfi, Da’u Fataken Dare, Dare Daya da dai sauran irin su sau bila adadin.Ya kamala karatun Sikandirensa a Sikandiren kimiyya ta gwamnati da ke Kafin Hausa a Jihar Jigawa a shekarar 1994. Ya samu shiga Makarantar Nazarin Addinin Musulunci da Shari’a ta Malam Aminu Kano (Legal), a nan ya samu shedar Diploma a kan Shari’a (Law) a shekarar 2003. Daganan ya wuce zuwa Jami’ar Bayero da ke Kano in da ya samu shedar samun Digiri na farko a fannin ilimin halayya da zamantakewar al’umma, (Sociology).. A yanzu haka kuma yana kan fara karatun Digirinsa na biyu a sabon zangon Karatu mai zuwa (2008/2009) a Jami’ar Bayero da ke Kano.

Zakariyya ya taba aikin kamfani a Kano da Legas a tsakanin shekarun 1995 zuwa 1999. Aikin da ya yi a Legas ya ba shi damar yin rubuce-rubuce a wasu fitattun jaridu na Kudancin Nijeriya kamar ‘The Punch’, ‘The Post Express’ da dai sauran irinsu. Haka kuma Zakariyya ya taba zama babban wakili (Bureau Chief) na Legas na kamfanin jaridar ‘The Shield Weekly’ da kuma Garkuwa da ke Kano. Ya taba zama wakilin Mujallar Fim a Kano. Hakanan kuma Marubuci na Musamman ga tsohuwar Mujallar ‘Mumtaz’ ta shahararren marubucin nan Ado Ahmad Gidan Dabino.

Zakariyya ya rubuta littattafai da kuma wakoki kirkirarru masu dama sai dai kuma ba’a taba buga ko daya daga ciki ba saboda wani shiri da yake da shi nan gaba (a shekarar 2009). Duk da haka a shekarar 2005 an juya littafinsa mai suna “Wuta a Masaka” zuwa fim mai taken “Wahami”, wanda darakta Ado Gidan Dabino ya bada Umarni. Zakariyya memba ne na Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen Jihar Kano. Ya na da mata da ya’ya biyu, kuma yanzu yana zaune a Kano.

Za a iya ziyartar blog din shi mai adireshi kamar haka http://www.zakariyyasarki.blogspot.com/
Ko kuma adireshin email : zakariyyasarki2005@yahoo.co.uk, zakariyyasarki@ymail.com
Lambobin Waya : 080-24388438, 064-893104, 064-317582.
** Mun buga wannan marubuci duk da cewa bai taba fidda littafi ba, bisa dalilai biyu, na farko dai mu kara masa kwarin gwiwa na biyu kuma tinda suna cikin na farko da suka turo ya samu wannan loto.

Thursday, September 11, 2008

BASHIR YAHUZA MALUMFASHI


An haifi Bashir Yahuza Malumfashi a ranar 15 ga watan Mayu na shekarar 1967 a garin Malumfashi, Jihar Katsina. Ya yi karatun firamare a Tunau Primary School, Unguwar Sodangi, Malumfashi, daga 1973 zuwa 1980. Daga nan ya wuce zuwa Government Day Secondary School, Malumfashi, daga 1981 zuwa 1986. Ya samu zuwa Kwalejin Share Fagen Shiga Jami'a (CAS, Zaria), daga shekarar 1987 zuwa 1989. Bai ci gaba da karatu ba saboda matsalar rashin lafiya da ta same shi, amma daga bisani ya shiga Kwalejin Horar da Jami'an 'Yan Sanda ta Kaduna (Police College, Kaduna), inda ya samu horo kan aikin 'yan sanda. Ya yi karatun Diploma a fannin Hikimar Koyar da Turanci (Diploma in Language Education, English) a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman Katsina. Haka kuma ya yi karatun Diploma kan ilimin sarrafa kalmomi (Diploma in Computer Data Processing) a wata makarantar Kwamfuta mai zaman kanta. Ya halarci kwasa-kwasai da tarukan kara wa juna ilimi a fannoni da dama. Ya fara aikin 'yan sanda ne a garin Dutsin-ma, Jihar Katsina, inda daga nan ya koma Kurfi, duk dai a Jihar Katsina. Daga bisani aka sake yi masa canjin wurin aiki zuwa Funtua, duk dai a Jihar Katsina. Ya samu canjin wurin aiki daga Funtua, aka mayar da ni zuwa Katsina. Daga nan ne aka mayar da shi aiki zuwa Abuja, inda na yi aiki a Babban Ofishin Binciken Laifuffuka na Hukumar 'Yan Sanda ta Kasa (Force Criminal Investigation Department), Area 10, Abuja. Mafi yawan aikinsa na 'yan sanda, ya yi shi ne a bangaren binciken laifuffuka da neman labarin sirri. A shekarar 2005 ne ya yi ritaya daga aikin 'yan sanda, bayan ya shafe shekaru 17 a kan aiki ke nan.

Ta bangaren harkar rubuce-rubuce kuwa, dama can shi mai sha'awar karance-karance da rubuce-rubuce ne. Ya fara rubutu tun yana aji uku a sakandare (1983), inda ya rubuta littafina na farko wanda ba a buga ba har yanzu. Sunan littafin Bak'i Da Fari, amma an karanta shi a Gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna, a filinsu na Shafa Labari Shuni. Daga nan ya ci gaba da rubuce-rubuce, ana bugawa a jaridun Hausa da na Turanci, musamman ma Gaskiya Ta Fi Kwabo, Nasiha, Almizan, Katsina News Week, New Nigerian, Weekly Trust, da sauransu. Littafinsa na farko da aka buga kuma ya fito kasuwa shi ne Babban Tarko, wanda ya fito a cikin shekarar 1997. Sai kuma na biyu mai suna Bak'in Kishi, wanda ya fito kasuwa a shekarar 2003. Yakan rubuta wakoki na Hausa da na Turanci, wadanda ake yawan bugawa a jaridu. Littafina da ke kan hanyar fitowa, shi ne Zinatu Matar Gwamna, wanda aka dade ana tsakura shi a cikin jaridar Aminiya.

A tarihin rubuce-rubuce, ya shiga gasar rubutu da dama, inda a shekarar 1995 da 1996 na samu kyaututtuka daga gidan rediyon Muryar Nijeriya, Lagos, a sakamakon zuwa na biyu da mukalolina suka a yi a shekarun na jere. A 2004 ma ya samu nasarar zuwa na daya a gasar rubuta labarai da gidan rediyon BBC suka sanya, mai taken Labarina.

Bayan ya yi ritaya daga aiki 'yan sanda a shekarar 2005, sai ya fada aikin jarida, inda ya ci gaba da aiki da Mujallar Fim, wacce dama na dade yana aika masu rubuce-rubuce tun daga fitowarta. Ya rike mukamin Manajan Edita na mujallar, inda ya zauna Kano. Daga baya ya koma Kaduna, inda ya fara aiki da jaridar Turanci mai suna Public Agenda, a matsayin Editan Shafukan Adabi. A cikin shekarar 2006 ne ya bar wannan jarida, ya koma aiki a kamfanin Media Trust Limited, masu wallafa jaridun Daily Trust, Weekly Trust, Sunday Trust da kuma Aminiya. A jaridar Aminiya nake, inda shi ne Editan Shafukan Adabi da Nishadi na jaridar, duk da cewa yakan taimaka da rahotanni ga sauran jaridun Turanci na kamfanin, daga lokaci zuwa lokaci.
A halin yanzu, yana da aure da 'ya'yaye. Babban burinsa a duniya shi ne, na son ya ga harshen Hausa ya bunkasa, ya zama babba a duniya; kamar kuma yadda yake son ganin cewa ya zama babban marubuci, don ba da gudunmowata ga al'umma.

Littattafansa na Hausa da suka fito sune:

1- Babban Tarko - 1997.
2- Bakin Kishi - 2003

http://us.f431.mail.yahoo.com/ym/Compose?To=byahuza03@yahoo.com
GSM: 08020968758, 08065576011.

Tuesday, September 9, 2008

MUHAMMAD LAWAL BARISTA

Muhammad Lawal Barista, Sakataren Kungiyar Inuwar Marubuta watau HAF sanannen marubuci ne kuma dan jarida wanda a halin yanzu yana karatu a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya na J amiár Bayero ta Kano. Mamba ne kuma na ANA Kano. Litattafansa na Hausa da aka buga sune:
Sakon Mutuwa
Makahon So
Buduri
Bakin Kishi
A Dalilin Talla…
TA Cuce Ni
Karshen So
Matan Zamani
Kasafi

SA'ADATU BABA AHMAD



Sa’adatau Baba Ahmad wadda makaranta suke fi sani da Ýar babanta na daya daga cikin fitattun marubuta mata na zamani. A halin yanzu tana karatun digiri na farko a jamiár Bayero ta Kano kuma jamiá ce a Kungiyar ANA Kano da kuma Hausa Authors Forum (HAF). Jerin litattafanta na Hausa da suke fito sune:

Wahala Siradin Rayuwa 1, 2
Yi Wa kai 1,2
Taka Tsantsan da Maza 1,2
Baram-Baram 1,2,3
Kishiya Ba Laifi Ba Ce 1,2,3
Rabon Bawa da Arziki
Mu Kame Kanmu
Auren Yanzu 1,2
Ban Karya Alkawari Ba 1,2,3
Zawaran Zamani 1,2,3
Kaddara ko Kishi 1,2
Birni da Kauye 1,2
Kantafi
Hasken Rana 1,2,3
Sirrin Zuciyata 1,2
Mutuwar Tsaye
Sallamar Bankwana
Zuciyar Kauna
Duhun Dare
Gudun Talauci