Wednesday, December 16, 2015

SABON LITTAFI: Ina farin cikin sanar da masu karatu fitowar wannan littafi nawa mai suna GUMAKAN ZAMANI. Ina fatan za a ji dadinsa. Na gode

Saturday, December 12, 2015

Ganawar Marubuci Farfesa Yusuf Adamu da daliban Kwalejin Sa’adatu Rimi


Published in AMINIYA NEWSPAPER on Friday, 24 July 2015 10:35
Written by Zaharaddeen Ibrahim Kallah

A Ranar Lahadi (12-7-2015), daliban Sashen Hausa na Kwalejin Sa’adatu Rimi suka karbi bakuncin Farfesa Yusuf M. Adamu, tsohon shugaban kungiyar Marubuta ta kasa (ANA) reshe Jihar Kano. Taron ya gudana ne bayan daliban da ke (part time) na kwalejin sun yi nazari a kan littattafin Farfesan mai suna Idan So Cuta Ne, wanda aka rubuta tun a shekara ta 1989.

Farfesa Yusuf Adamu na rubutu cikin harshen Hausa da Turanci, ya fitar da littattafai masu yawa wadanda suka hada da Ummul-Khairi da Maza Gumbar Dutse da Gumakan Zamani. A littattafansa na Turanci akwai Butterfly and Other Poems da Animal in the Neighbourhood da Landscapes of Poetry da They Can Speak English da A flat World da sauransu.
Taron ya kayatar matuka, domin ba ya ga marubucin, wasu daga cikin marubuta sun halarta wadanda suka hada da Zaharaddeen I. Kallah da Dokta Faruk Sarkin Fada da Kabiru Yusuf Anka. Sannan akwai da yawa daga cikin malaman Sashin Hausa na kwalejin, karkashin jagorancin Shugabar Sashin, Dokta Bilkisu Yusuf, wadda Dokta Mahe Isa Ahmed ya wakilta.
A yayin jawabin maraba, Dokta Mukhtar Sadauki ya sanar da cewa wannan rana ita ce rana ta karshe da daliban suka gama daukar darasi a kan wannan fanni, hakan yasa suka gayyaci marubucin littafin da aka nazarta wato Farfesa Yusuf M. Adamu don ya amsa tambayoyi daga daliban.



Farfesa Yusuf Adamu ba boyayye ba ne a bangaren rubuce-rubuce, domin yana daga cikin jiga-jigan da suka haifar da Adabin Hausa na zamani. Tun bayan da kamfanin wallafa littattafai na NNPC ya dakatar da buga littattafan Hausa, marubuta na wannan zamani suka shiga mawuyacin hali na rashin samun kafar da za su isar da sakonninsu. A cikin wannan hali ne marubuta irin su Talatu Wada da Farfesa Yusuf Adamu da Ado Ahmad Gidan Dabino da Sunusi Shehu Daneji da dan’Azimi Baba da su Balaraba Ramat da su Adamu Muhammad da Alkhamees D. Bature da Bala Anas Babinlata da sauransu suka jagoranci nakudar Adabin Hausa na zamani. Hakika zan iya cewa gudunmawarsu ta taka rawa wajen dawwamar da Adabin Hausa har ya zama a raye zuwa wannan lokaci. A yau idan ana maganar marubutan da suke rubutu cikin harshen uwa, yana cikin wadanda suka yi fice. Wannan abin alfahari ne ga duk mai kishin yare da al’ada ta Hausa.
Farfesa Yusuf, yayin gabatar da tarihinsa da tarihin fara rubuce-rubucensa, ya gabatar da yadda ya fara sha’awar sauraron labarai da tatsuniyoyi, wadanda sun taimaka wajen zamansa marubuci. A cewarsa, mahaifinsu kan dauke su lokacin hutu zuwa wasu garuruwa, inda bayan sun dawo yakan ummarce su da su rubuta abin da suka gani. Da haka ya fara rubutu, inda ya rubuta littafinsa na farko Maza Gumbar Dutse, sai kuma Idan So Cuta Ne… da ya rubuta shi a cikin mako guda. A cewarsa, har yakan zana yadda yake son wani abu daga cikin bayaninsa ya kasance ya yi rubutu.

Hakika wannan dan gajeran tarihi zai haska wa wadanda suke da sha’awar zama marubuta da su yi koyi da shi, su fahimci suna da baiwar rubutu. Na san da yawa daga cikin mutane suna da wannan baiwa amma ba su sani ba. Misali, akwai mutane da idan suna ba ka labari sai ka rantse suna nan aka yi abu, ko kuma ka ga wadanda ke da sha’awar sauraron tatsuniyoyi da labarai, babu shakka hakan na nuna cewa za su iya zama kwararrun marubuta.

Kamar yadda na ce a baya, taron ganawa da daliban ya yi armashi kwarai, domin ya ba su dama sun yi tambayoyi ga Farfesa sannan sun gana da wasu daga cikin marubutan Hausa. Hakan ya sa an yi musayar ra’ayi da fito da wasu muhimman bayanai a kan adabi. Daga cikin abubuwan da aka duba sun hada da alakar marubuci da labarin da ya rubuta. Wasu daga cikin mahalarta taron sun yi duba ga wannan bangare. Misali, marubucin Idan So Cuta Ne… dan boko ne wanda ya kai matsayin Farfesa, hakan ya yi tasiri a cikin littafinsa na amfani da ’yan boko a cikin taurarin labarinsa. Kusan kowa yana yin boko, illa wasu kalilan da ba ’yan boko ba wadanda su ma sun taka rawa wajen fito da jigon labarin.
An kawo misalai na Abdulmalik da Salisu da Zairo a wasu daga cikin ’yan book, sai kuma Hajiya Bilkisu a matsayin wadda ba ta yi boko ba, kuma hakan ya kawo matsala ga Abdulmalik da Farida a kan soyayyarsu.

Daga cikin abubuwan da daliban suka tambaya, har da abin da ya ja hankalin marubucin ya yi wannan littafin. Yayin ba da amsa, marubucin ya ce ya jima yana jin ana maganar duk wata soyayya da aka jima ana yi a karshe zai yi wuya a yi aure. Kasancewar yana da wacce yake so kuma sun jima tare sai ya fara tunanin abin da zai faru idan haka ta faru, wannan ne ya sa ya fara tunanin yadda zai ba kansa hakuri. Wannan ne ya sa ya rubuta littafin Idan So Cuta Ne…daliban sun yaba wa marubucin a kan cewa an rubuta littafin tun 1989 amma sai a dauka a wannan lokaci aka rubuta shi. An kuma yaba masa yadda littafin ya kasance tsaftatacce da al’umma za su amfana da shi.


Sauran baki su ma sun tofa albarkacin bakinsu a kan taron. A nasa bangaren, Zaharaddeen Kallah ya nuna farin cikin kasancewa a wurin taron, musamman saboda sha’awa da daliban suka nuna na nazarin Adabin Hausa. Ya kuma ba su shawara da su yi alfahari da harshen Hausa wanda a halin yanzu ya dauki hanyar shahara sosai a fadin duniya. Ya nemi daliban su kasance masu dabi’ar karance-karance da nazarin littattafai, wanda hakan zai taimaka musu matuka, musamman ga wadanda ke da sha’awar zama marubuta.

Dokta Faruk Sarkin Fada kuma ya yaba wa Sashen Hausa na kwalejin saboda wannan abu da suka shirya wanda zai taimaka wa daliban a cikin karatunsu. Ya yi kokarin fahimtar da daliban tasirin rubutu, musamman da aka samu wata daga cikin daliban marubuciya ce. A cewarsa yana da kyau mutum ya yi rubutu ba kawai don abin da zai samu ba, sai don manufarsa a rubutu wanda ilmantarwa da gyara al’umma ke ciki. Ya ce da yawa daga cikin marubuta sai sun bar duniya sannan rubutunsu ke shahara. Ya ba da misali da Muhammad Ikbal daga tsohuwar kasar Indiya da Pakistan wanda rubutunsa ya yi tasiri wajen kawo juyin juya hali a kasar Iran, bayan tsawon lokaci da rasuwarsa. Duk da cewa Ikbal bai taba zuwa Iran ba, rubutunsa da aka fassara ya yi tasiri sosai a can. Wannan ya sa a yanzu har maulidinsa suke gudanarwa saboda jin dadin abin da rubutunsa ya yi. Daga karshe sai Dokta Faruk ya ba da gudunmowar littattafansa guda uku da ya buga da Hausa ga Sashen Hausa na kwalejin.

Taron ya zo karshe da jawabin godiya daga bakin Dokta Mahe Isa Ahmed, wanda ya gode wa Farfesa Yusuf Adamu saboda lokacinsa da ya ba da na amsa gayyatarsu. Ya kuma gode wa sauran marubuta da suka halarci taron, a inda ya nuna aniyar sashen na kulla alaka da kungiyar Marubuta ta Najeriya (ANA) reshen Jihar Kano don ciyar da adabi gaba.
Hakika wannan alaka da kwalejin marubuta za su yi farin ciki da ita, musamman don za ta kasance hanya da za a taimaki juna. A bangaren dalibai zai kasance hanyar nazari da horar da su a harkar nazari tare da ganawa da marubuta. A bangaren marubuta da suke bukatar manazarta don rubutunsu ya ci gaba da rayuwa, su ma abin alfahari ne. Tabbas wannan yunkuri abin maraba ne musamman a wannan lokaci da ake neman yin wancakali da koyar da harshen Hausa a makaratun sakandire na kasar nan, wanda haka kan iya kawo barazana ga harshen gaba daya.


Zaharaddeen Ibrahim Kallah, tsohon sakataren kungiyar Marubutan ta Najeriya ne reshen jihar Kano, sannan ma’aikaci a Jami’ar Bayero, Kano. dinik2003@yahoo.co.uk This email address is being protected from spambots. You need JavaScript enabled to view it.

Wednesday, November 27, 2013

DR ALIYA ADAMU AHMAD



Dr Aliya Adamu Ahmad na daya daga cikin matasan mata manazarta a Nazarin Hausa. Ta samu digirinta na farko da na biyu daga Jami'ar Usmanu Danfodiyo Sokoto. Ta kuma samu digirinta na uku daga Jami'ar Bayero ta Kano. Ta koyar a Shehu Shagari College of Education Sokoto. A halin yanzu tana koyarwa a Sokoto State University, kuma ita ce shugabar Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Taken aikin digirinta na uku shi ne: “Rupert Moultrie East: Gudummuwarsa ga Adabin Hausa, da Kuma Sharhi Kan Ayyukansa”. Ta kuma gabatar da makalu a tarrurruka da dama. An kuma buga wasu takardunta a mujallun ilmi da littattafai. A shekarar 2012 ta je SOAS ta Jami'ar London inda ta yi zaman bicike a matsayin Leventis scholar. Tana da aure da yaro.

Thursday, March 10, 2011

JIYA BA YAU BA

A wannan hoto ana iya ganin shahararren marubucin Hausa na zamani Muhammad Lawan Barista (Hagu) da Mashahurin mawakin Hausa Aminuddeen Ladan Abubakar ALA (Dama) a wani taro da ANA Kano da hadin gwiwar Kano State Library Board suka shiryawa marubuta a 2003.

TUNA BAYA

Allahu Akbar. Wannan hoton Marigayi Bashari Farouk Roukbah ne (hagu) da Marigayi Hadi Abdullahi Alkanci (dama) a shekarar 2003 lokacin da ANA Kano da hadin gwiwar Kano State Library Board suka shirya taron sanin makamar aiki ga marubutan Hausa.

Tuesday, November 2, 2010

MARUBUTA A AL’UMA

Dk. Yusufu M Adamu
Shugaban ANA Reshen Jihar Kano.
Kasancewarta makala da aka gabatar a Taron Sanin Makamar Aiki na Marubutan Hausa na Kasa wanda Kungiyar Marubuta ta Nijeriya Reshen Jihar Kano da hadin gwiwar Hukumar Dakunan Karatu ta Jihar Kano suka shirya. Yuli 1st -2nd, 2004 a Dakin Karatu na Murtala Mohammed, Kano.


Wannan take da nake son yin Magana a kansa take ne mai ma’ana a taro irinb wannan saboda sa ran da ake yi zai nunawa marubuci ko marubuciya matsayinsa a cikin al’umar da Allah ya halicce shi. Take ne da ake san ran zai fadakar da marubuci ko marubuciya hakkoka da suka rataya a kansu da kuma manufar tasirin abubuwan da suke rubutawa.



Babu al’uma da za ta ci gaba matukar bat a da marubuta. Marubuta sun eke tattara tarihin al’umarsu su adana shi ta hanyar rayayyen adabi. Wasu daga cikinsu ana haihuwarsu ne da baiwar rubutu, wasu kuma kan same ta saboda kokarinsu da kuma dagewa. Duka wadannan rukunai na marubuta bas u iya yin rubutu har sai suna da baiwa ko sun samu baiwa. Amma duka za mu kira sun e marubuta.



Marubuta sun banbanta da sauran mutane ba wai domin sun fi sub a, sai don kawai Allah ya huwace musu wata hanya ta tunani wadda wanda ba marubuci ba, ba shi da ita. Marubuta na yin tunani ne na daban tare da kallon rayuwa da al’amuran da kan je su komo da wata fahimta ta daban. Su kan yi amfani da haruffa zuwa kalmomi da jimloli zuwa shararori domin bayyana tunaninsu wanda zai iya zama tamkar tafsiri ne na rayuwar da suka kalla suke aiki a kan ta.



Marubuci ya banbanta da masanin tarihi domin shi marubucin tarihi na bayyana hakikanin abubuwan da suka faru ne bayan ya tabbatar da afkuwarsu. Masanin tarihi kuma bay a maida hankali a kan kowa da kowa, face wadanada suka yi fice. Saboda haka hanyar da akan bi domin fahimtar yaya al’uma ta rayu a wani zamani shi net a yin nazarin kirkirarrun ayyuka da suka yi a zamaninsu. A nan marubucin zube ko wake ko wasan kwaikwayo kan rubuta wani abu da ya shafi mai mulki da talakansa, mai arziki da mara shi, kyakkyawa da mummuna, mai addini da mara shi, mai azama da malalaci, samari da ‘yan mata, tsofaffi da kananan yara, dabbobi da aljanu da dai sauransu. A cikin irin wadannan ayyuka na adabi ne za a iya fahimtar yadda wani ko wata suka rayu . Misal ga wani wake nan da wani Fir’auna ya rubuta na yabon Ubangiji fiye da shekaru 3000 da suke shude:

Ayyukanka suna da yawa matuka

Ya ubangiji tilo, babu wani tamkar sa

Kai ka hallici duniya yadda ka so

Da kai kadai ne tilo,

Duk mutum, duka dabbobi na gida da na dawa

Duk hallitta mai tafiya bisa dugaduganta

Duk abubuwan dake sama da halittu masu fiffike suna tashi



Kai ka halicci kasashe har da kasar Masar

Ka ajiye kowane mutum a wuri nasa daban

Al’umomi suna harsuna daban daban

Siffarsu ta jiki da launi sun banbanta

Domin ka banbance tsakaninsu.



Daga wannan wake na yabon Ubangiji za mu iya fahimtar yadda Misrawan Dauri a wancan lokaci suka fahimci Ubangiji da yadda tsarin addininsu yake. Ba wannan ne kawai misali ba, akwai misalai da dama da za a iya kawowa daga rubuce-rubucen al’umomi daban daban na duniya. Ko nan in muka dawo gida, za mug a cewa in mun karanta littatafan su Abubakar Imam muka hada su da na su Bashari Farouk Roukbah muka kuma karanta litattafan su Hafsatu AbdulWaheed da na su Ado Ahmad Gidan Dabino, za mu iya bada bayani akan yadda rayuwar Bahaushe ta sauya dangane da al/ada da kuma ma harshe. Idan kana nazarin harshe, babu yadda za a yi ka ga an yi amfani da wasu kalmomi ko an bas u wata ma’ana sai dai-dai zamanin da aka soma hakan. Misali in kana karanta Ruwan Bagaja za ka ga ana amfani ne da famai-famai in ana maganar kudi. Idan ka zo ka na karanta littafi na zamani za ka ga an yi amfani da wata kalma wadda a litattafan baya ba za a bata ma’anar da aka bat a a littafi na yau ba. Alal misali;

“Ka share ta kawai” ko

“Ta na ja masa aji”

Marubuci kan iya jawowa al’umarsa ci aba ko dakushewa kuma matukar ba a fahimci manufar marubuci ba, to ka jahilci fahimtarsa, sai dai kuma shi abu na adabi da zarar marubuci ya fito da shi ya zama mallakar duniya ba tasa ba. Wannan ya sa kowa zai iya fassara rubutu da iya tasa fahimtar wadda ba lallai net a zama ta dace da ainihin abinda shi marubucin ke nufi ba. Babu ja a wannan fuska. A wasu lokuta kuma akan yi dace wurin fadar ainihin manufar marubuci. Ta kowace hanya muka duba dai, rubutu na fita daga ma’anar da marubuci ya ba shi da zarar an fitar da shi. Wannan ya say a zama wajibi marubuci da ke yi wa al’umarsa rubutu ya yi kokarin yi ta yadda manufarsa a ta fito karara kuma a fahimce ita.



Shin wai wanene marubuci? Zai yi matukar wahala a bayyana a bayyane ma’anar ko wanene marubuci. Sai dai wannan ba zai hana mu jarraba bada ma’ana ga kalmar marubuci ba. A tawa fahimta wadda tsukakkiya ce ana iya cewa marubuci mutum wanda kan yi amafani da basirar da Allah ya ba shi ta hanyar kirkirar wani yanani na gasket ko na almara ko wani tunani ko fahimta ta domin gina wasu mutane ko ma’anoni domin isar da wani sako ga al’uma ta zamansa da wadda za ta zo bayansa. MArubuci kan tsara wanann sako nasa ta hanyar mai jan hankali da kuma dadin lafazi tare da cusa kwarewar harshe da yi masa adon da zai sa mai karatunsa ya kusanta da shi ya so shi ya kuma sa mai karatunsa ya rika jin kamar abin da yake karantawa hakika ne. Wannan yana faruwa ne saboda marubuci kan yi amfani da mutane da wurare da ta’adodi da harshe da fahimta irin ta mutanen da ake rubutu dominsu.



Marubuci kan iya yin rubutu domin dalilai masu dama ko wani hali da ya samu kansa ko dai wata manufa. Don haka, marubuci kan iya yin rubutu domin nishadantarwa ko ilmantarwa ko wayar da kai ko farfaganda ko zambo ko neman kudi ko neman suna ko tada zaune tsaye ko yada wata akida da ya yarda da ita ko gina wata manufa ko rusa ta ko domin tabbatar da al’uma a wani tabbataccen ra’ayi. Ko kuma ya yi rubutu wai don rubutu kawai. Marubuci kan yi iyaka kokarinsa wurin shawo kan mai karatu ya yadda ya amince ya kuma hakkake cewa wannan sako nasa gaskiya ne, amintacce ne kuma dauwamamme mai farin jinni.



Wannan ya say a zama wajibi ga al’uma ta dage ta yi tasiri mai kyau ga marubutan da ke cikinta domin yin tasiri ga tunaninsa ta yadda shi kuma zai sarrafa tunaninsa wurin yin rubuce-rubuce da za su dace da al’umarsa su kuma ciyar da ita gaba ba tare da an rika samun tangarda ba. Shi rubutu tamkar kashi ne ko amai, in ka ci zogala sai ka yi kashi bakikkirin in ka ci doya sai ka yi aman kura-kuran doya haka in wake ka ci.



Shi kuma marubuci ya zama lazim ya fahimci cewa zama marubuci al’amari ne babba domin kuwa yana tatatre da hakkoki da nauye-nauye. Na farko marubuci a kodayaushe kokari yake yi ya fahimci al’umarsa. Na biyu duk lokacin da yake tunani dole ne ya rika sanya tunaninsa da mutuntakarsa a ma’auni. A cikin rubutunsa zai iya zama na kwarai ya kuma zama baragurbi, ya zama namiji ya zama mace, ya zama yaro ya zama babbaa da dai sauransu. Wannan na faruwa ne aboda duk lokacin da ya so rubuta wani abu game da wani jinsi ko ajin mutane sai ya yi tunani irin nasu. Abu na uku ba zai san iya tasirin da rubutunsa zai yi ba bayan ya fito da shi. Wannan ya say a zama wajibi marubuci ya tabbatar da cewa al’uma ta tsira daga dafin alkalaminsa ta kuma amfana da rahamar tawwadar alkalaminsa. Duk abinda mutum zai rubuta ya yi tunanin irin tasirin da zai iya jawowa ga al’uma mai kyau ko mara kyau. Wannan ya say a zama dole marubuci musulmi ya yi fancakali da manufar nan ta cewa wai marubuci na da ‘yancin rubuta binda ya ga dama kuma ana yin rubutu ne kawai don rubutu. Ana yin rubutu ne da manufa, kuma ga marubuci musulmi dole ta zama manufa Islamiyya.



Marubuci kan iya zama tamkar dan liken asiri saboda dole sai ya yi bincike mai zurfi akan abinda yake rubutawa in dai har yana so ya rubuta adabi mai rai kuma ingantacce tabbatacce. Idan wani ya gamu da marubuci a wani wuri da yake ganin bai dace ba, zai iya zarginsa da batanci, amma ba lallai bane cewa batanci yaje yi, kila bincike ya je yi. Idan ka ga marubuci a mashaya ko gidan karuwai ko kuwa tare da ‘yan kwaya ko ‘yan daba, bincike na iya kai shi. Da zarar ya fahimci yadda rayuwar wadanda yake so ya yi rubutu a kansu in ya yi maka rubutu sai ka ranstse shi ma dan cikinsu ne. Idan muka karanta littafin Bala Anas Babinlata Sara da Sassaka sai mu rantse Bala ya zauna a Afirka ta Kudu. In ka karanta Karshen Alewa na Marigayi Bature Gagare sai ka ranste tsohon dan tawaye ne, haka in ka karanta ‘Yar Tsana na Ibrahim Sheme sai ka rantse tsohon dan dandi ne. Bincike ne ya bas u wannan dama.



Ta yaya basirar kirkira marubuciya ko marubuciya ke zuwa? Basirar marubuci kan z one ta hanyoyi da dama. Wasu daga zurfin tunani wasu daga karanta ko ganin wani abu wasu kuma daga faruwar wani abu. Ko dai yaya basirar ke zuwa tana samo tushe ne daga al’amuran dan adam na yau da gobe. Gina labarin ko wasan kwaikwayo ko wake kuma kan samu net a hanyar tattara manufar jigon wuri guda tamkar yadda mai zane zanen gine-gine kan yi dan karami. Wasu tun farko su kan san inda labarinsu ko wakensu ya nufa, wasu kuma sai a hankali suke gina shi ta hanyar ba shi kansa labarin dama ya sauya ta yadda al’amura suka kasance. Misali lokacin da na yi tunanin rubuta Idan So Cuta Ne, tun farko na san yadda zan gina labarin da yadda zai kare. Labari ne na wani saurayi da wata budurwa da suka so junansu matukar so amma ba za su yi aure ba, sai dai diyansu za su yi aure. Wannan shine dunkulalliyar manufar Idan So Cuta Ne amma warware jigon ya dauki lokaci. Na dauki lokaci ina ta gina labarin a a kaina ina rubuta wasu abubuwa ina Tarawa. Na dauki lokacin wurin tunanin a wadanne garuruwa zan gina labarin? Su wa da w azan sa a labarin? Wadanne sunaye ne za su dace da kowane tauraro, babba da karami? Yaya ta’ada da salon maganar kowane daga cikinsu za ta kasance da sauransu. Bayan duk na gama wannan aiki na zauna cikin mako guda na rubuta Idan So Cuta Ne.



Wannan ya kawo mu maganar lokacin yin rubutu. Da wane lokaci ake yin rubutu kuma tsawon wane lokaci ya kamata marubuci ya kamata ya dauka kafin y agama wani aji na rubuitu? Ta wannan fuska babu amsa guda daya. Lokacin yin rubutu ya dangantaka ya kuma bambanta daga marubuci zuwa marubuci. Wani kan yi rubutu duk lokacin da ya ga dama, wani sai rubutun ya zo masa don kansa wani kuma kan fara rubutu daga ganin faruwar wani abu ko kuma wani abu ya harzuko shi. Amma dangane da lokaci na rana ko dare, kowane marubuci na da lokacin da yake rubutu. Wasu kuma kan yin me kawai duk lokacin da abin ya zo musu. Dangane da tsawon lokacin da ya kamata a dauka kuwa shi ma ya bambanta da abubuwa da dama. Na farko kaifn basirar marubuci da kwarewarsa. Na biyu sanin abinda zai yi rubutu a kai ciki da waje. Na uku mutuntakarsa, kodai ta zumudi ce ko jirgin dankaro ko kuma madaidaiciya.



A nan ya kamata in yi kira ga al’umarmu da bat a dauki marubuta da muhimanci da da su sauya ra’ayi. A karshe zan iya cewa dan abinda na iya kalatowa kalilan ne daga kalilan dangane da taken wannan makala sai a yi hakuri. Amma zan rufe da tunatar da mu cewa rubutu tamkar shuka ce wanda in hart a girma za ta baka inuwa kuma ka ci ‘ya’yanta. Yana kuma iya zama tamkar dan kunama ko abinda Hausawa ke kira “kaikayi koma kan mashekiya. Rubutu rayyayyen al’amari ne wanda kan wanzu matukar wanzuwar duniya.



Assalamu Alaikum.

Wednesday, March 31, 2010

FAUZIYYA D. SULAIMAN


Fauziyya D. Sulaiman wadda aka fi sani da Matar Bello Q far Q an haife ta a unguwar Fagge a Shekarar 1981 ta yi karatuna na Firamare a Makarantar Festival Primary School, daga nan wuce makarantar ‘yammata ta kwana Government Girls Secondary School ‘Yar gaya a shekara ta 1993, bayan ta kammala karatunta na Jiniya ta koma Makarantar Government Girls College Dala ta karasa karatunta daga 1995 zuwa 1998. Daga nan ta yi aure a shekara ta 1999. A shekara ta 2003 ta koma karatu a Makarantar College of Health Sciences, School of Hygiene in da ta yi Diploma a kan Assistant Nutritionist. Daga nan ta yi Certificate a Makarantar School of Management, akan Hotel and Catering Services.

A game da rubutu kuwa ta fara rubuta littafi a shekarar 2002, in da littafi na farko mai suna Me na yi mata?. Daga nan ta ci gaba da rubuta littafi da suka hada da:

Kishin Banza
Guduna Ake yi
Rayuwar ‘Ya Mace
Mece ce Rayuwa
Burin Raina
Karshen Wahala
Labarin Zuciya
Matsalar Mace
Mijin Uwa
Auren Kudi
Duk Abinda Namiji Ya yi


Fauziyya mamba ce a Kungiyar Marubuta ta Najeriya reshen jihar Kano kuma tana rike da mukamin jami’a a majalisar gudanarwa ta Kungiyar tun watan Maris na 2009 har zuwa 2010. Daga nan aka sake zabenta a dai wannan mukami daga watan Maris na 2010 har zuwa watan Maris na 2012 insha Allahu.

Wednesday, February 24, 2010

FATIMA UBA ADAMU (ZAHRA)


An haifi Fatima Uba Adamu a Kano. Ta yi karatun Firamare a Tarauni Special Primary School daga 1988-1994, ta yi Sakandare a Makarantar Sakandaren 'Yanmata ta Kabo daga 1996-2001. Daga 2002 zuwa 2006 ta yi digirinta na farko a fannin Hausa, a halin yanzu tana digirinta na biyu tare da kwarewa a fannin Adabin Hausa. Ta kuma yi difiloma a fannin kwamfyuta. Ta dan taba aiki da jaridar Daily Trust kafin ta koma karatunta na digiri na biyu. Littafinta na farko shi ne Kaddara Da Zabi.

Thursday, February 4, 2010

Marubutan Hausa a Yamai

Wannan hoton Dr Yusuf Adamu ne (dama) da Ado Ahmad Gidan dabino (Hagu) suka yi shigar buzaye a lokacin da suka kai ziyara Yamai da marubutan Hausa na Nijeriya.

FARFESA IBRAHIM MALUMFASHI

Farfesa Ibrahim Malumfashin na daga cikin fitattu kuma Zakakuran manazartan Adabin Hausa.

Monday, October 19, 2009

TA'AZIYYAR HADI ABDULLAHI ALKANCI



Hagu zuwa dama: Danjuma Katsina, Hadi Alkanci, Yusuf Adamu a wani taro a Kano


Allah ya yi wa Marubuci Hadi Abdullahi Alkanci rasuwa ranar Litinin 12 ga Oktoba 2009 a Sakkwato bayan ya sha fama da rashin lafiya. Rasuwar Alkanci babban rashi ne ga marubuta da manazarta da ma al'umar Nijeriya. Allah ya jikansa da gafara ya kuma albarkaci bayansa.
Bayan sanarwar da na yi a dandalin marubuta kamar haka:

Salam,Ina bakin cikin sanar da ýan uwa cewa Allah ya yi wa Hadi Abdullahi Alkanci rasuwa jya da yamma a Sakkwato, ya yi fama da rashin lafiya wajen watannin uku, mun yi rashi babba, muna kuma rokon Allah ya gafarta masa ya kuma jikansa da rahma amin. Muna rokon yan uwa su yi masa addu'a koyaushe, ga dan takaitaccen tarihinsa nan a wannan rariyar likau
http:// marubutanhau sa.blogspot. com/2008/ 09/hadi-abdullah i-alkanci. html

Allah ya gafarta masa ya kuma sa mu ma mu cika da imani amin. Dr Yusuf Adamu

Mun samu sakwannin taáziyya da dama, ga kalilan daga cikinsu a kasa:

Ado Ahmad Gidan Dabino
ALLAH AKBAR, Allah ya ji kan Hadi Abdullahi Alkanci. Marubucin Soyayya Ta Fi Kudi (littafin wasan kwaikwayo) da Harsashin Kasa da Shin So Gaskiya Ne? da sauran su. Babu shakka mun yi babban rashi a fagen marubuta, haziki gwarzo a fagen fasaha ya tafi.

Ba zan manta da haduwa ta ta karshe da Hadi ba a lokacin da ya zo Kano wajen bikin kaddamar da littattafan Bashir Othman Tofa, yana cikin mutanen hudu da na yi hira da su a ciki shirin da nake gabatarwa a gidan rediyo FREEDOM mai suna Alkalami Ya Fi Takobi, mutane sun yaba da ire-iren bayanan da ya yi sosai, kuma in yana magana lallai ka san cikakken mutumin Sokoto ne, mai iya karin magana da dabarun zance.Lokacin da na ji labarin rasuwarsa ta hanyar SMS daga Yusuf Adamu ina jihar Lagos, ba shakka na kadu sosai da ganin wannan sakon.

ALLAHU AKBAR! ALLAHU !! AKBAR!!! Allah ka rahamshe shi, ka sa ya huta, mu kuma Allah ya kyauta tamu in ta zo. Allah ka sa gidan Aljanna ce makomarmu baki daya. Amin!!! Ina mika sakon gaisuwa ga dukkanin 'yan'uwa da abokan arziki da dukkan Sakkwatawa.


***
JAMILU NAFSENCIBIYAR LAFAZIN HAUSA
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJI' UN....Aduk sa'ilin da muka ji wannan kalma tuni take mana nuni da wani gagarumin abu ne ya auku.hakanne yasa nima ina samun wannan rashin jangwarzo mai bada gudunmawa musamman aharkar wasanni, abunda na iya furtawa kenan tare da tawassali da cewa muma tamu tananan zuwa. sai dai muce ubangiji ya kai rahma agareshi. mu kuma Allah yasa mu cika da imani, amin.

*****
Mamane Sahabi Ousmane Alias M.SONiamey Niger
Allahu akbar haka ne, Allah yaji kanshikuma ya sa, ya huta.abida ya bari Allah yabasu hakurida masoya da kuma yan uwa. mu kuma da muka rage in tamu ta zoAllah ya sa, mugama da iskan duniya lafiya Amin.ita rayuwa haka take, kowa lokacin shi, zai jira.ba'a gaggauta wa kowa, kuma ba'a jinkirta wa kowa. kulli nafsi za'ikatil mautko wace rai! sai ta dan-dana mutuwa.gaba dayan mu, muci gaba da yi wa junan mu, addu'a.intamu ta zo, Allah ya sa mucika da kalmar La'ilaha illallah Muhammadu Rasulullah.

******

Sarkin yan Nijar,
Atta Oumaten
إنا لله وانا اليه راجعون منهـا خلقناكم وفيهـا وعيدكم ومنهـا نخرجكم تارةاخرى
Dawannan nake meka tsakon ta'aziyar daukacin yan Nijar dake cikin wadannan zauruka, ga iyalai da abokan arziki na wannan ba wan Allah, allah yasa ya huta mu kuma idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani.
***
Uba Dan Zainab
Allah yayimasa rahama yasada shi da annabi sallalahu alaihi wasallamzuriyarsa kuma Allah yashiga lamuransu yasakasu bin surad'al mustaqeem.

****
Ahmad Yahuza Getso (B.A. MIAD, MPPA, HPDCS)
Allah ya gafarta masa ya kyautata tamu.
***
Muhammad Muhammad
Allah ya gafarta masa, mu kuma Allah ya kyauta karshen mu.
***
Isa Muhammad Inuwa
Allah Ya jikan Babban Marubuci Hadi Alkanci, Ya sa mutuwa hutu, Ya kyauta namu zuwan, Ya sa mu je a sa'a. Amin!

****
Muhammad Mansoor
Allah ya sa ya huta amin suma amin.
****
Ibrahim Sheme
Allah Ya jikanshi, ya yi masa rahama. Allahu Akbar! One of the last Titans of Classic Hausa Literature. Wallahi mun yi rashi.
****
Bala Muhammad (A Daidaita Sahu)
Innalillahi Wa inna Ilaihir Raji'un. Allah ya jikansa ya gafarta masa. In tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani, amin.

****
Aisha Zakari
Allah ya jikansa ya gafarta masa, lallai kam mun yi babban rashi.
****
Dr Wale Okediran (ANA President)
May his soul rest in perfect peace, amin.
***
Danjuma Katsina
A gaskiya mun yi rashi babba, Allah ka jikan wannan bawa naka ka gafarta masa amin.
***
Alhaji Kabiru Katsina
Allah ya gafarta masa, mun yi rashin jagora a rubutu.
***
Dr. Aliya Adamu
Allah ya Jikansa ya gafarta masa amin.

NASIRU G AHMAD YANAWAKI

An haifi Nasiru G. Ahamd a unguwar ‘Yan Awaki cikin Birnin Kano, ran 6 ga Safar, 1384, BH. (4/2/1964). Bayan karatun Alkur’ani, ya yi makarantar Firamare Islamiyya ta ‘Yan Awaki, daga 1975-1981. Ya wuce zuwa makarantar Nazarin Addinin Musulunci mai zurfi ta Shahuci (1981-1985). Sai Makarantar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Aminu Kano, (1986-1989) inda ya samu diploma a Harsunan Hausa da Larabci da Nazarin Addinin Musulunci. Daga (1993-1996), ya je Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo ta Sakkwato, inda ya samu digirin farko a harshen Hausa.
A shekarar 1984, ya halarci ajin koyon buga keken rubutu (Typewriting) da ke karkashin Hukumar Yada Ilimin Manya ta Kano, a 1992, ya halarci wani kwas da Jami’ar Musulunci ta Madina ke shiryawa, don horar da malaman Arabiyya da addinin Musulunci, a Jami’ar Bayero ta Kano. A 1992 din dai, ya je wani kwas na addinin Musulunci, a garin Idah, cikin jihar Kogi. A 1999, ya yi wani kwas na karatun gida, karkashin “Sincere Writers Club”, inda ya samu takardar shaida (certificate) kan aikin jarida.
A 1991, ya je jihar “Cross Rivers” inda ya yi aikin jami’i mai duba Malaman Kidaya (Supervisor). Ya koyi sarrafa na’ura mai kwakwalwa a aikace, (Practical) a “Urgent Computers” inda ya taba yin aiki. Yana cikin masu duba wakar Hausa, ta jarrabawar ‘W.A.E.C.’ Wakili ne na jaridar “People And Events”. Editan littattafai ne mai zaman kansa. Ya yi aikin koyarwa a makarantu da dama, (Firamare da Sakandare) tun daga 1984 zuwa yanzu. Yana da sha’awar ziyarce-ziyarce da kulla abota, da karance-karance a kowane fannin ilimi da rayuwa. Ya rubuta litattafai da dama, da wakoki jingim. Nasiru kuma na cikin Sahún gaba na ‎ ‘yan Kungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen jira Kano. A halin yanzu yana karatun digirinsa na biyu a Jamiár Ahmadu Bello (ABU) Zaria.

Monday, June 22, 2009

MUHAMMAD USMAN


Muhammad Usman wanda kuma aka sani da Sunusi Shehu Daneji na daya daga cikin turakun da su assassan adabin Hausa na zamani. Marubuci, mai dab'i kuma mai wallafa mujallar Hausa. Marubuci ne wanda ya ci gaba da bada jagora ga marubutan Hausa na zamani tare da kokarin samar da adabi mai tarbiyya. Yana rubuce-rubuce na tarbiyya da kimiyyar sararin samaniya da sauransu. Cikin litattafansa akwai:

Bankwana da Masoyi

Yaron Kirki

Madubin Imani

HAFSATU AHMAD ABDULWAHID


An haifi Hajiya Hafsatu a Birnin Kano. Ta yi karatunta na boko a Kano kafin ta yi aure ta koma Gusau da zama. Fitacciyar marubuciyar Hausa ce wadda littafinta na So Aljannar Duniya shi ne littafin zube na farko da mace ta rubuta a harshen Hausa. Ta wallafa 'Yardubu Mai Tambotsai da kuma Saba Dan Sababi. Tana kuma rubutu da turanci da kuma fillanci. Marubuciya ce wadda ke da kishin rubutu ta kan kuma halarci tarurrukan marubutan Hausa da na Nijeriya. Bayan rubutu takan taba siyasa don ta taba takarar Gwamna a jihar Zamfara.

Sunday, June 14, 2009

BASHIR OTHMAN TOFA



Fitaccen dan siyasa kuma hamshakin dan kasuwa wanda kuma ya yanke shawarar yin amfani da basirar da Allah ya yi masa ya zama marubuci. Bashir Tofa ya yi rubuce-rubuce da harshen Hausa bisa zabin ciyar da harshen gaba. Ya wallafa litattafan Hausa da dama wadanda suka hada da na kirkira da kuma na ilmi. Cikin litattafansa da suka fito sun hada da:

Amarzadan a Birnin Aljanu
Amarzadan da Zoben Farsiyas
Kimiyyar Sararin Samaniya
Tunaninka Kamanninka
Kimiyya da Al'ajaban Al-Qur'ani
Gajerun Labarai
Mu Sha Dariya
Rayuwa Bayan Mutuwa

Saturday, June 13, 2009

BINTA RABIÚ SIPIKIN



(Za mu kawo bayanai a kanta bada jimawa ba)

UMMA SULAIMAN 'YAN AWAKI


Fitacciyar marubuciyar Hausa Umma Sulaiman 'Yan Awaki... (za mu kawo bayanan nan gaba kadan)

UMMA ADAMU


An haifi Umma Adamu ranar 15th ga Oktoba 1981 a Gwarzo, duk da cewa ita 'yar asalin Hadejia ce. Ta yi karatun Firamare a Kanti Primary School Kazaure daga 1987-2003. Ta kuma yi karatun

Sakandare a Malam Madori da Sakandaren Kimiyya ta Taura inda ta gama a 1999. Ta ci gaba da karatu daga 2000 a School of Health Technology Jahun da Informatics Institute Kazaure da kuma Jigawa State College of Education har zuwa 2006. A halin yanzu (2009) tana karatu ne a Kano State University of Science and Technology Wudil. Cikin litattafan da ta buga sun hada da:

1. Raino, 2. Rigakafi 3. Sirrinus ko Sirrimu 4. Wahayi 5. Zaman Jira 6. Ya Zalince ni 7. Sabanin Ra'ayi 8. Abu a Duhu.

Tana sha'awar koyarwa da kallon fina-finai da tafiye-tafiye da koyarwa da kuma rubuta kirkirarrun labaru.

Wednesday, May 20, 2009

HIRA DA YARON MALAM

Daga Maje El-Hajeej <sirrinsu@yahoo. com>


Nine Bajakaden Abubakar Imam. Cewar Yaron Malam. Tun lokaci da shahararren marubucin da a yau duniyar hausawa ke girmamawa a matsayin kakan marubuta ya amsa kira zuwa ga mahaliccinsa, manazarta suka dukufa domin zurfafa nazarin gano ko wanene zai gaji shi marigayin, tare da rike alkalaminsa ga ci gaba da assasa yanayi da kuma salonsa na imamantar da labari zuwa yadda zai dace da Hausawa da kuma al’adunsu. Musamman ma ko domin dinbim amfanin da a yau littattafansa ke dasu ga dalibai sakamakon sanya su da ake yi a manhajar karatu, da kuma zama tushe da suke yi na fara koyon karatu ga mafi yawancin garuruwan Hausawa.

Duk da dai wannan bakin gumurzu ne, wanda sai an samu sadauki mai akwatin siddabaru, ko kuma yakau dan mayakiya da zasu ja tunga, su kuma yi shahada, sannan su fara fafatawa suyi gumu gami da artabu tamkar a tsibirin Bamuda da yahudu badda musumi. Domin ba aiki ne na mata ba, ballantana gimbiya Assadatu ko Bajakadiya ko kuma Mayakiya suyi hargagagin farawa. Amma Abdullahi Mukhtar da ake yiwa lakabi da Yaron Malam, ya sanya sulke tare da daura damarar karbar wannan garkuwa ta Imam kamar yadda ya bayyanawa wakilinmu Maje El-Hajeej Hotoro.

(An yi wannan tattaunawa da shine a watan Janairun 2007)

Zamu fara da jin tarihinka. Sunana Abdullahi Mukhtar Yaron Malam, an kuma haife ni a 1976 a unguwar Fagge dake karamar hukumar Fagge Kano. Na kuma yi karatun firamare na a Fagge Special daga 1984 zuwa 1988. Inda na karasa karatun firamarena a Gama Sabuwa saboda komawa can da muka yi. Dagan nan kuma ban samu damar ci gaba da karatuna ba, sai aka kaini makarantar allo a garin Hadeja. Wacce ban dade ba aka dawo dani, sakamakon rashin lafiya da na yi, inda na ci gaba da karatun allo. Kafin daga baya na shiga makarantar koyom larabci ta Aliyu Bn Abu Thalib, wacce daga baya aka mayar da ita Umar Bn Khattab dake Gyadi-gyadI a nan Kano daga 1994 zuwa 1999. Lokaci guda kuma ina mai ci gaba da halartar karatun azure. Na sake shiga makarantar koyon larabci ta Rasulul Akram, bayan na kamala na tafi Irshadul Umma Islamic College ta Shahuci da ake kira da Aliya daga 2001 zuwa 2004. Wanda a halin yanzu ina jami’ar Bayero, inda nake karanta aikin jarida. Tare da dan hadawa da kasuwanci.

Shin ko a wacce shekara ka fara rubutu, kuma ko menene ya dauki hankalinka har ka shigo fagen?
Alal hakika zan iya cewa tun farko na taso ne da sha’awar rubuce-rubuce, domin tun ina firamare na kan dauki takarda nayi ta kwafar littafin Baba da Inna da kuma Iliya dan mai karfi a cikin littattafan makaranta na. Sannan kuma ni dama makaranci ne na littattafan labaran Larabci da Hausa. Kamar irinsu Magana Jar ice, Yawon Duniyar Haji Baba, Labaran Da da na Yanzu, da sauransu. Domin ko a lokacin da na ke makarantar Allo, ragowar ’yan uwana almajirai kan zagaye ni na rika basu labarin wani littafi dana karanta. Na fara fitar da littafina na farko ne a 1999 wanda na addini ne mai suna Hukunce-hukuncen Azumi da Addu’o’in Watan Ramadan. Sai kuma Hukunce-hukuncen Jinin Haila, amma ban fitar dashi ba, sai bayan da na fitar da littafina mai suna kissoshin Ahlul Baiti. Dagan an kuma sai na fitar da Bajakade da kuma sirrin aure da ma’aurata, wadanda sune litattafan da suka zama sanadiyyar aka anni a duniyar marubuta.

A halin yanzu ko littattafanka sun kai nawa?
Zuwa yanzu na samu nasarar rubuta littattafai da dama kamar, Bajakade, Mayakiya, Bakin gumurzu, Gimbiya Assadatu, Artabu, Fafatawa, Gumu, Tsiburin Bamuda, Sadauki mai akwatin siddabaru, Tunga, Shahada, Bajakadiya, ‘Yar mai ganye, Yakau dan mayakiya da kuma Yahudu badda Musulmi da kuma na addini da dama.

Ko da wane irin salo kake amfani a rubutunka?.
Salon rubutuna sune salon jarumta, abin dariya, soyayya da kuma hikimar Magana. Jigo kuma shine karfafa akidar addinin musulunci, tsayar da adalci da kuma kyautata zamantakewa tsakanin al’ummar musulmi da kuma wadanda ba musulmi ba.

Mafi yawancin irn wadannan littattafai da suke dauke da abubuwan da ka rubuta akan samu fassarowa ake daga wasu littattafai, shin naka ma fassara ne ko kuma kirkirowa kake yi?
Maganar gaskiya ina kirkirar labari na ne, kuma mafi yawanci duk wanda ya dauko wani littafi ya fassara, sai an samu wasu sun daga sun ce ga daga inda ya fassaro. Amma ni babu wanda zai daga littattafaina yace ga daga inda na fassaro. Sai dai ina karance-karance kamar yadda na fada domin kaifafa basirar da Allah Ya yi min, wanda dama ita baiwa ce, amma ilimi, bincike da kuma tambaya akan abin day a shigewa mutum duhu, sune abincin basira. Sannan juya ilimi daga wani harshen zuwa wani ba laifi bane, matukar anyi hakan ta halattacciyar hanya ba satar fasaha ba.

Ko me zaka iya cewa dangane da kalaman Dakta Malumfashi da kuma na Farfesa Abdallah da suka bayyana cewa nan gaba zaka iya gadar Marigayi Abubakar Imam a fagen rubutu?
Wannan ba a bin mamaki bane idan aka yi la’akari da yanayi da kuma salonsa na ban dariya da dabarun zaman duniya da kuma hikimar Magana. Kana kuma yana gina labarin san e akan sigar zamanin da, sannan wani lokaci yak an jefa soyayya. To idan akayi la’akari da yanayin rubuce-rubucena salon da nake bi kenan. Kumai an matukar samun karfafawa akan wannan salon rubutu nawa, domin farfesa Abdallah yak an kira ni da sabon Abubakar Imam. Sannan musamman ya zaunar dani ya bani labarin dabarun da marigayin ke bi a rubutunsa. Sannan akwai Malam B.K Zariya wanda sunyi zamani da Marigayi Imam, shima takanas yakan kirani ya zaunar dani ya sanar dani tarihin yadda rayuwar Abubakar Imam ta kasance, harma yakan kirani da marigayi Imam.

Shin ko akwai wata kyauta da makarantanka suka taba yi maka wacce ba zaka taba mantawa da ita ba?.
Akwai wata a Bauchi da ta taba yi min kyautar Alqur’ani mai girma, wacce a gaskiya bazan manta da wannan kyautar ba. Sannan kuma masoya daga wurare daban-daban, suna yi min fatan alheri wanda wannan ma babbar kyauta ce, dab a zan manta da ita ba.

Ko a wane irin yanayi ka fi son yin rubutu?
Ina yin rubutu a kowane irin yanayi, amma nafi jin dadin yanayin bayan sallar asuba. Amma a yanzu na dauki wani salo nana yin rubutu a bakin ruwa, ko cikin daji mai bishiyu da kuma ciyayi, ko wajen gari kamar yadda Abubakar Imam ya yi.

Ko shin a matsayinka na dan kasuwa yaya kake hada harkar rubutu da kuma kasuwanci lokaci guda?.
Ai shi rubutu baya hana marubuci yi wasu abubuwan yau da kullum. Misali idan ka dauki marigayi Imam malamin malakaranta ne kuma marubuci lokaci guda. Sannan daga bisani ya zama Editan wata jarida, wanda a wannan lokacin babban aiki ne saboda karancin kayan aiki. Haka ma a yau zaka samu marubuta suna kuma wasu abubuwa na daban, ciki hard a sojoji da ‘yan sanda da sauran ayyukan gwamnati ko kuma na kamfani kuma wannan baya hana su rubutu.

Da kayi maganar kasuwanci sai ka tuno da korafin da wasu marubuta ke yi na matsalar ‘yan kasuwa, wajen rashin sakar musu kudadensu da wuri bayan an sayar da kayansu.?
Lallai kam wannan matsala ce da muka dade muna kuka da ita, amma yanzu alhamduLillahi al’amura sun fara kyautata, domin zaka samu mud a kanmu marubutan muna yabon wasu ‘yan kasuwar da kokarin bayar da kudI akan kari. Su kuma wadanda ake samun jinkirin sun dauki alwashin magance hakan. Sannan kuma kungiyar masu littattafai da kuma ‘yan kasuwa, suna aiki tukuru wajen ganin ta magance wannan matsala. Mu kara hakuri nan ba jimawa ba, komai zai zama tarihi Insha Allahu.

Kwanakin baya kungiyar marubuta ta kasa reshen jihar Kano (ANA) ta jagoranci marubutan Hausa wata tafiya zuwa kasar Nijar. Kasancewar kana cikin shugabannin wannan kungiya, ko wadanne matsaloli da kuma nasarori kuka samu yayin wannan tafiya.?
Makasudin wannan tafiya shine ziyara da kuma taron karawa juna sani tsakanin marubutan Nijeriya da kuma na waccan kasa. Kana kuma da yin bincike akan yanayin zamantakewa da al’adunsu domin samun karin gogewa ga marubutanmu na nan. Matsala kadai da muka samu ita ce ta motarmu da ta lalace, wanda hakan ya tilasta mana yin amfani da guzurinmu domin kara hayar wata motar da ta karasa dam u can. Mun kuma samu nasarori sosai musamman ma na karawa juna sani, sannan ga kuma ziyarar muhimman wurare da muka yi, sun kuma karrama mu sosai domin hidimomi da suka yi man na tsaro da kuma makwanci. Sannan kuma mun fa’idantu matuka gaya , basirarmu ta kara fadada, wanda dama masu hikima sunce tafiya mabudin ilimi.

TA'AZIYYAR YARON MALAM

Allah ya yi wa Abdullahi Muktar Yaron Malam rasuwa ranar Lahadi 17 ga Mayu 2009 da misalin sha biyu na rana, a dakin Karatu na Muratala Muhammad dake birnin Kano. Ya rasu ya bar mata daya da diya uku. Fitaccen marubuci, shugaban Brigade Authors Forum (BAF) kuma jami'i a Kungiyar Marubuta ta Nigeria (ANA) reshen Jihar Kano, Yaron Malam marubuci ne ingarma wanda ya bada muhimmiyar gudunmuwa wurin ci gaban adabin Hausa. Yaron Malam kuma mawallafi ne kuma mai sayar da littattafai. Mun yi babban rashi. Allah ya jikan Yaron Malam ya gafarta masa amin.


Dr Yusuf M Adamu
Shugaban ANA Kano

Dannan wannan rariyar likau don karanta takaitaccen tarihin Abdullahi Muktar Yaron Malam: http://marubutanhausa.blogspot.com/2009/02/abdullahi-mukhtar-yaron-malam.html